< Karin Magana 7 >

1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
Mon fils, garde mes paroles et cache par-devers toi mes commandements.
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Garde mes commandements, et tu vivras, – et mon enseignement, comme la prunelle de tes yeux.
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Lie-les sur tes doigts, écris-les sur la tablette de ton cœur.
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Dis à la sagesse: Tu es ma sœur! et appelle l’intelligence ton amie;
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
pour te garder de la femme étrangère, de la foraine qui use de paroles flatteuses.
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
Car, à la fenêtre de ma maison, je regardais à travers mon treillis,
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
et je vis parmi les simples, j’aperçus parmi les jeunes gens, un jeune homme dépourvu de sens,
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
qui passait dans la rue, près du coin où demeurait cette femme, et il prit le chemin de sa maison,
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
au crépuscule, au soir du jour, au sein de la nuit et de l’obscurité.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
Et voici, une femme [vint] à sa rencontre, ayant la mise d’une prostituée et le cœur rusé.
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
Elle était bruyante et sans frein; ses pieds ne demeuraient pas dans sa maison,
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
elle était tantôt dehors, tantôt sur les places, et guettait à tous les coins.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
Et elle le saisit, et l’embrassa, et d’un visage effronté lui dit:
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
J’ai chez moi des sacrifices de prospérités, j’ai aujourd’hui payé mes vœux;
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
c’est pourquoi je suis sortie à ta rencontre pour chercher ton visage, et je t’ai trouvé.
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
J’ai étendu sur mon lit des tapis, des couvertures de fil d’Égypte de couleurs variées;
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
j’ai parfumé ma couche de myrrhe, d’aloès, et de cinnamome.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
Viens, enivrons-nous d’amours jusqu’au matin, délectons-nous de volupté;
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
car [mon] mari n’est pas à la maison, il s’en est allé loin en voyage;
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
il a pris un sac d’argent en sa main, il viendra à sa maison au jour de la pleine lune.
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
Elle le détourna par beaucoup de douces paroles, elle l’entraîna par la flatterie de ses lèvres.
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
Il est allé aussitôt après elle, comme le bœuf va à la boucherie, et comme les ceps [servent à] l’instruction du fou,
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
jusqu’à ce que la flèche lui transperce le foie; comme l’oiseau se hâte vers le piège et ne sait pas qu’il y va de sa vie.
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
Maintenant donc, fils, écoutez-moi, et soyez attentifs aux paroles de ma bouche.
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Que ton cœur ne se détourne pas vers ses voies, et ne t’égare pas dans ses sentiers;
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
car elle a fait tomber beaucoup de blessés, et ceux qu’elle a tués sont très nombreux.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)
Ce sont les voies du shéol que sa maison; elles descendent dans les chambres de la mort. (Sheol h7585)

< Karin Magana 7 >