< Karin Magana 7 >
1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
My son, keep my words, and lay up my commandments with thee.
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Keep my commandments and live, and my law as the apple of thine eye.
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Bind them upon thy fingers. Write them upon the tablet of thy heart.
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Say to wisdom, Thou are my sister, and call understanding thy kinswoman,
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
that they may keep thee from the interloping woman, from the stranger who flatters with her words.
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
For at the window of my house I looked forth through my lattice,
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
and I beheld among the simple ones, I discerned among the youths, a young man void of understanding
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
passing through the street near her corner. And he went the way to her house,
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
in the twilight, in the evening of the day, in the middle of the night and in the darkness.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
And, behold, there met him a woman attired like a harlot, and wily of heart.
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
She is loud and headstrong. Her feet abide not in her house.
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
Now she is in the streets, now in the broad places, and lies in wait at every corner.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
So she caught him, and kissed him. With an impudent face she said to him,
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
Sacrifices of peace offerings are with me. I have paid my vows this day.
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
Therefore I came forth to meet thee, diligently to seek thy face, and I have found thee.
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
I have spread my couch with carpets of tapestry, with striped cloths of the yarn of Egypt.
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
I have perfumed my bed With myrrh, aloes, and cinnamon.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
Come, let us take our fill of love until the morning. Let us solace ourselves with love.
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
For the man is not at home. He has gone a long journey.
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
He has taken a bag of money with him. He will come home at the full moon.
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
With her much fair speech she causes him to yield. With the flattering of her lips she forces him along.
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
He goes after her straightaway, as an ox goes to the slaughter, or as a fool to the correction of the stocks,
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
till an arrow strikes through his liver, as a bird hastens to the snare. And he does not know that it is for his life.
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
Now therefore, ye sons, hearken to me, and attend to the words of my mouth.
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Let not thy heart decline to her ways. Go not astray in her paths.
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
For she has cast down many wounded. Yea, all her slain are a mighty host.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )
Her house is the way to Sheol, going down to the chambers of death. (Sheol )