< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
HIJO mío, si salieres fiador por tu amigo, si tocaste tu mano por el extraño,
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
Enlazado eres con las palabras de tu boca, y preso con las razones de tu boca.
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Haz esto ahora, hijo mío, y líbrate, ya que has caído en la mano de tu prójimo: ve, humíllate, y asegúrate de tu amigo.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
No des sueño á tus ojos, ni á tus párpados adormecimiento.
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
Escápate como el corzo de la mano [del cazador], y como el ave de la mano del parancero.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Ve á la hormiga, oh perezoso, mira sus caminos, y sé sabio;
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
La cual no teniendo capitán, ni gobernador, ni señor,
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
Prepara en el verano su comida y allega en el tiempo de la siega su mantenimiento.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
Perezoso, ¿hasta cuándo has de dormir? ¿cuándo te levantarás de tu sueño?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un poco de sueño, un poco de dormitar, y cruzar por un poco las manos para reposo:
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
Así vendrá tu necesidad como caminante, y tu pobreza como hombre de escudo.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
El hombre malo, el hombre depravado, anda en perversidad de boca;
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
Guiña de sus ojos, habla con sus pies, indica con sus dedos;
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
Perversidades hay en su corazón, anda pensando mal en todo tiempo; enciende rencillas.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
Por tanto su calamidad vendrá de repente; súbitamente será quebrantado, y no [habrá] remedio.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
Seis cosas aborrece Jehová, y aun siete abomina su alma:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
Los ojos altivos, la lengua mentirosa, las manos derramadoras de sangre inocente,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
El corazón que maquina pensamientos inicuos, los pies presurosos para correr al mal,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
El testigo falso que habla mentiras, y el que enciende rencillas entre los hermanos.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Guarda, hijo mío, el mandamiento de tu padre, y no dejes la enseñanza de tu madre:
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
Atalos siempre en tu corazón, enlázalos á tu cuello.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
Te guiarán cuando anduvieres; cuando durmieres te guardarán; hablarán contigo cuando despertares.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
Porque el mandamiento es antorcha, y la enseñanza luz; y camino de vida las reprensiones de la enseñanza:
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
Para que te guarden de la mala mujer, de la blandura de la lengua de la extraña.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
No codicies su hermosura en tu corazón, ni ella te prenda con sus ojos:
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
Porque á causa de la mujer ramera [es reducido el hombre] á un bocado de pan; y la mujer caza la preciosa alma del varón.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
¿Tomará el hombre fuego en su seno, sin que sus vestidos se quemen?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
¿Andará el hombre sobre las brasas, sin que sus pies se abrasen?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
Así el que entrare á la mujer de su prójimo; no será sin culpa cualquiera que la tocare.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
No tienen en poco al ladrón, cuando hurtare para saciar su alma teniendo hambre:
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
Empero tomado, paga las setenas, da toda la sustancia de su casa.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
Mas el que comete adulterio con la mujer, es falto de entendimiento: corrompe su alma el que tal hace.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
Plaga y vergüenza hallará; y su afrenta nunca será raída.
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
Porque los celos son el furor del hombre, y no perdonará en el día de la venganza.
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
No tendrá respeto á ninguna redención; ni querrá [perdonar], aunque multipliques los dones.

< Karin Magana 6 >