< Karin Magana 6 >
1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
Hijo mío, si saliste fiador por tu prójimo, Si empeñaste tu palabra a un extraño,
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
Si te enredaste con tus palabras, Y quedaste atrapado con los dichos de tu boca,
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Haz esto ahora, hijo mío, y líbrate. Ya que caíste en las manos de tu prójimo: Vé, humíllate e importuna a tu prójimo.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
No concedas sueño a tus ojos, Ni adormecimiento a tus párpados.
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
Líbrate como gacela de la mano [del cazador], Como un ave de la trampa.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Mira a la hormiga, oh perezoso, Observa sus caminos y sé sabio,
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
La cual, sin tener jefe, Ni gobernador, ni soberano,
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
Prepara en el verano su comida. En el tiempo de la cosecha guarda su sustento.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
¿Hasta cuándo estarás acostado, oh perezoso? ¿Cuándo te levantarás de tu sueño?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un rato duermes, otro dormitas, Un rato cruzas los brazos y descansas.
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
Te llega la miseria como un vagabundo, Y tu necesidad como un hombre armado.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
Hombre depravado es el hombre inicuo, Que anda en la perversidad de su boca,
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
Guiña con un ojo, menea los pies, Hace señas con los dedos.
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
En su corazón hay perversidades, Maquina maldades, y continuamente busca rencillas.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
Por tanto, su calamidad vendrá de repente. Súbitamente será quebrantado y no habrá remedio.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
Seis [cosas] aborrece Yavé, Y aun siete repugna su alma:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
Ojos altivos, boca mentirosa, Manos que derraman sangre inocente,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
Corazón que maquina planes perversos, Pies presurosos para correr al mal,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
Testigo falso que habla mentiras, Y el que enciende discordias entre sus hermanos.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Hijo mío, guarda el mandamiento de tu padre, Y no abandones la instrucción de tu madre.
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
Átalos continuamente a tu corazón, Enlázalos en torno a tu cuello.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
Cuando camines, te guiarán. Cuando duermas, te protegerán. Hablarán contigo al despertar.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
Porque el mandamiento es lámpara, La enseñanza es luz Y camino de vida las reprensiones de la instrucción.
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
Te guardarán de la mala mujer, De la blandura de la boca de la mujer extraña.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
No codicies en tu corazón su hermosura, Ni dejes que te cautive con sus párpados.
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
Porque si la prostituta busca una hogaza de pan, La adúltera caza una vida preciosa.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
¿Tomará el hombre fuego en su seno, Sin que ardan sus ropas?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
¿Andará un hombre sobre brasas, Sin que se quemen sus pies?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
Así sucederá con el que se une a la mujer de su prójimo. Ninguno que la toque quedará impune.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
¿No desprecian al ladrón aunque robe Para llenar su estómago cuando tiene hambre?
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
Si es sorprendido, tiene que pagar siete veces Y entregar todo lo que tiene en su casa.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
Pues el adúltero es hombre sin cordura, Destructor de sí mismo es el que lo hace.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
Heridas y deshonra hallará, Y su afrenta no será borrada.
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
Porque los celos son la ira del hombre. En el día de la venganza no perdonará,
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
Ni aceptará algún rescate. No se aplacará aunque ofrezcas muchos regalos.