< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
ای پسرم، اگر ضامن کسی شده و تعهد کرده‌ای که او قرضش را پس بدهد،
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
و اگر با این تعهد، خود را گرفتار ساخته‌ای،
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
تو در واقع اسیر او هستی و باید هر چه زودتر خود را از این دام رها سازی. پس فروتن شو و نزد او برو و از او خواهش کن تا تو را از قید این تعهد آزاد سازد.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
خواب به چشمانت راه نده و آرام ننشین،
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
بلکه مانند آهویی که از چنگ صیاد می‌گریزد یا پرنده‌ای که از دامی که برایش نهاده‌اند می‌رهد، خود را نجات بده.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
ای آدمهای تنبل، زندگی مورچه‌ها را مشاهده کنید و درس عبرت بگیرید.
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
آنها ارباب و رهبر و رئیسی ندارند،
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
ولی با این همه در طول تابستان زحمت می‌کشند و برای زمستان آذوقه جمع می‌کنند.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
اما ای آدم تنبل، کار تو فقط خوابیدن است. پس کی می‌خواهی بیدار شوی؟
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
کمی خواب بیشتر، کمی چُرت بیشتر، کمی دست رو دست گذاشتن و استراحت بیشتر،
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
و فقر و تنگدستی همچون راهزنی مسلح به سراغ تو خواهد آمد.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
آدم رذل و خبیث کیست؟ آنکه دائم دروغ می‌گوید،
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
و برای فریب دادن مردم با چشمش چشمک می‌زند، با پایش علامت می‌دهد، به انگشت اشاره می‌کند،
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
و در فکر پلید خود پیوسته نقشه‌های شرورانه می‌کشد و نزاع بر پا می‌کند.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
بنابراین، ناگهان دچار بلای علاج‌ناپذیری خواهد شد و در دم از پای در خواهد آمد و علاجی نخواهد بود.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
هفت چیز است که خداوند از آنها نفرت دارد: نگاه متکبرانه، زبان دروغگو، دستهایی که خون بی‌گناه را می‌ریزند، فکری که نقشه‌های پلید می‌کشد، پاهایی که برای بدی کردن می‌شتابند، شاهدی که دروغ می‌گوید، شخصی که در میان دوستان تفرقه می‌اندازد.
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
ای پسر من، اوامر پدر خود را به جا آور و تعالیم مادرت را فراموش نکن.
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
سخنان ایشان را آویزه گوش خود نما و نصایح آنها را در دل خود جای بده.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
اندرزهای ایشان تو را در راهی که می‌روی هدایت خواهند کرد و هنگامی که در خواب هستی از تو مواظبت خواهند نمود و چون بیدار شوی با تو سخن خواهند گفت؛
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
زیرا تعالیم و تأدیب‌های ایشان مانند چراغی پر نور راه زندگی تو را روشن می‌سازند.
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
نصایح ایشان تو را از زنان بدکاره و سخنان فریبنده‌شان دور نگه می‌دارد.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
دلباخته زیبایی این گونه زنان نشو. نگذار عشوه‌گری‌های آنها تو را وسوسه نماید؛
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
زیرا زن فاحشه تو را محتاج نان می‌کند و زن بدکاره زندگی تو را تباه می‌سازد.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
آیا کسی می‌تواند آتش را در بر بگیرد و نسوزد؟
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
آیا می‌تواند روی زغالهای داغ راه برود و پاهایش سوخته نشود؟
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
همچنان است مردی که با زن دیگری زنا کند. او نمی‌تواند از مجازات این گناه فرار کند.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
اگر کسی به دلیل گرسنگی دست به دزدی بزند مردم او را سرزنش نمی‌کنند،
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
با این حال وقتی به دام بیفتد باید هفت برابر آنچه که دزدیده است جریمه بدهد، ولو اینکه این کار به قیمت از دست دادن همهٔ اموالش تمام شود.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
اما کسی که مرتکب زنا می‌شود احمق است، زیرا جان خود را تباه می‌کند.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
او را خواهند زد و ننگ و رسوایی تا ابد گریبانگیر او خواهد بود؛
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
زیرا آتش خشم و حسادت شوهر آن زن شعله‌ور می‌گردد و با بی‌رحمی انتقام می‌گیرد.
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
او تاوانی قبول نخواهد کرد و هیچ هدیه‌ای خشم او را فرو نخواهد نشاند.

< Karin Magana 6 >