< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
Mon fils, si tu t’es porté garant pour ton prochain, si tu as engagé ta parole pour un étranger,
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
tu es pris au piège de tes promesses; tu es devenu le prisonnier de ta parole.
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Fais donc ceci, mon fils, pour recouvrer ta liberté, puisque tu es tombé au pouvoir d’autrui: va, insiste avec énergie et livre un assaut à ton prochain.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
N’Accorde pas de sommeil à tes yeux ni de repos à tes paupières.
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
Dégage-toi, comme le cerf de la main du chasseur, comme le passereau de la main de l’oiseleur.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Va trouver la fourmi, paresseux, observe ses façons d’agir et deviens sage:
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
elle n’a ni maître, ni surveillant, ni supérieur;
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
et elle prépare sa nourriture durant l’été, elle amasse ses provisions au temps de la moisson!
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
Jusqu’à quand, paresseux, resteras-tu couché? Quand sortiras-tu de ton sommeil?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
"Ah! dormir encore un peu, rester un peu assoupi, entrelacer un peu les mains pour reposer!"
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
Cependant, la pauvreté s’introduit chez toi comme un rôdeur, et la misère comme un guerrier armé.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
Un personnage ignoble, un homme inique, c’est celui qui a recours au langage tortueux,
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
qui cligne des yeux, frappe des pieds, fait des signes avec ses doigts,
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
et, le cœur plein d’artifices, passe son temps à méditer le mal, à déchaîner la discorde.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
Aussi le malheur fond-il soudain sur lui; d’un coup, il est brisé et sans retour.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
Il est six choses que l’Eternel déteste et sept qu’il a en horreur:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
les yeux hautains, la langue mensongère, les mains qui répandent le sang innocent;
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
le cœur qui ourdit des desseins pervers, les pieds impatients de courir au mal,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
le faux témoin qui exhale le mensonge, enfin l’homme qui déchaîne la discorde entre frères.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Mon fils, sois fidèle aux recommandations de ton père, ne délaisse pas l’enseignement de ta mère.
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
Porte-les constamment attachés à ton cœur, noués à ton cou.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
Qu’ils te guident dans tes marches, veillent sur ton repos et te soient un sujet d’entretien à ton réveil.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
Car le devoir est un flambeau, la doctrine une lumière, les dictées de la morale un gage de vie.
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
C’Est ainsi que tu seras protégé contre la femme vicieuse, contre la langue mielleuse de l’étrangère.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
Ne convoite pas sa beauté en ton cœur, ne te laisse pas prendre à la séduction de ses paupières.
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
Car pour une courtisane on peut être réduit à une miche de pain; une femme adultère prend dans ses filets un gibier de prix.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
Peut-on attiser du feu dans son sein, sans que les vêtements soient consumés?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
Peut-on marcher sur des charbons ardents, sans se brûler les pieds jusqu’au vif?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
Il en est ainsi de celui qui approche de la femme de son prochain; il ne restera pas indemne, celui qui la touche.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
On ne méprise pas le voleur qui commet un larcin pour assouvir sa faim.
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
Mais s’il est pris, il devra payer au septuple, donner tous les biens de sa maison.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
Commettre un adultère c’est être insensé qui veut se perdre agit ainsi.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
Il ne recueillera que souffrances et déshonneur; sa honte sera ineffaçable.
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
Car la jalousie exaspère la fureur du mari: il sera sans pitié au jour de la vengeance.
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
Il ne se laissera apaiser par aucune rançon; il se montrera inexorable, dusses-tu prodiguer les présents.

< Karin Magana 6 >