< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
Mon fils, si tu t’es porté caution pour ton prochain, si tu as engagé ta main pour un étranger,
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
tu es enlacé dans les paroles de ta bouche, tu es pris dans les paroles de ta bouche.
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Mon fils, fais donc ceci, et délivre-toi, puisque tu es tombé en la main de ton prochain: va, humilie-toi, et insiste auprès de ton prochain.
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
Ne permets pas à tes yeux de dormir, ni à tes paupières de sommeiller;
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
dégage-toi, comme la gazelle, de la main [du chasseur], et comme l’oiseau, de la main de l’oiseleur.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Va vers la fourmi, paresseux; regarde ses voies, et sois sage.
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
Elle qui n’a ni chef, ni surveillant, ni gouverneur,
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
elle prépare en été son pain, elle amasse pendant la moisson sa nourriture.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
Jusques à quand, paresseux, resteras-tu couché? Quand te lèveras-tu de ton sommeil?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un peu de sommeil, un peu d’assoupissement, un peu croiser les mains pour dormir…,
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
et ta pauvreté viendra comme un voyageur, et ton dénuement comme un homme armé.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
Celui qui marche, la perversité dans sa bouche, est un homme de Bélial, un homme inique;
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
il cligne de ses yeux, il parle de ses pieds, il enseigne de ses doigts;
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
il y a des pensées perverses dans son cœur, il machine du mal en tout temps, il sème des querelles.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
C’est pourquoi sa calamité viendra subitement; il sera tout à coup brisé, et il n’y a pas de remède.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
L’Éternel hait ces six choses, et il y en a sept qui sont en abomination à son âme:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
les yeux hautains, la langue fausse, et les mains qui versent le sang innocent,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
le cœur qui machine des projets d’iniquité, les pieds qui se hâtent de courir au mal,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
le faux témoin qui profère des mensonges, et celui qui sème des querelles entre des frères.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Mon fils, garde le commandement de ton père, et n’abandonne pas l’enseignement de ta mère;
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
tiens-les continuellement liés sur ton cœur, attache-les à ton cou.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
Quand tu marcheras, il te conduira; quand tu dormiras, il te gardera; et quand tu te réveilleras, il s’entretiendra avec toi.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
Car le commandement est une lampe et l’enseignement une lumière, et les répréhensions de la discipline sont le chemin de la vie,
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
pour te garder de la mauvaise femme, des flatteries de la langue d’une étrangère.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
Ne désire pas sa beauté dans ton cœur, et qu’elle ne te prenne pas par ses paupières;
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
car par la femme prostituée [on en vient] jusqu’à un morceau de pain, et la femme d’autrui chasse après l’âme précieuse.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
Un homme prendra-t-il du feu dans son sein sans que ses vêtements brûlent?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
Si un homme marche sur des charbons ardents, ses pieds ne seront-ils pas brûlés?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
Ainsi celui qui entre vers la femme de son prochain…, quiconque la touchera ne sera point innocent.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
On ne méprise pas un voleur s’il vole pour satisfaire son âme quand il a faim;
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
et s’il est trouvé, il rendra le septuple, il donnera tous les biens de sa maison.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
Celui qui commet adultère avec une femme manque de sens; celui qui le fait détruit son âme:
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
il trouvera plaie et mépris, et son opprobre ne sera pas effacé;
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
car dans l’homme, la jalousie est une fureur, et il n’épargnera pas au jour de la vengeance;
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
il n’acceptera aucune propitiation, et ne se tiendra pas pour satisfait, quand tu multiplierais les présents.

< Karin Magana 6 >