< Karin Magana 6 >

1 Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
My son, if thou be surety for thy friend, thou hast engaged fast thy hand to a stranger.
2 in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
Thou art ensnared with the words of thy mouth, and caught with thy own words.
3 to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
Do therefore, my son, what I say, and deliver thyself: because thou art fallen into the hand of thy neighbour. Run about, make haste, stir up thy friend:
4 Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
Give not sleep to thy eyes, neither let thy eyelids slumber.
5 Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
Deliver thyself as a doe from the hand, and as a bird from the hand of the fowler.
6 Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
Go to the ant, O sluggard, and consider her ways, and learn wisdom:
7 Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
Which, although she hath no guide, nor master, nor captain,
8 duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
Provideth her meat for herself in the summer, and gathereth her food in the harvest.
9 Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
How long wilt thou sleep, O sluggard? when wilt thou rise out of thy sleep?
10 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Thou wilt sleep a little, thou wilt slumber a little, thou wilt fold thy hands a little to sleep:
11 talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
And want shall come upon thee, as a traveller, and poverty as a man armed. But if thou be diligent, thy harvest shall come as a fountain, and want shall flee far from thee.
12 Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
A man that is an apostate, an unprofitable man, walketh with a perverse mouth,
13 wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
He winketh with the eyes, presseth with the foot, speaketh with the finger.
14 wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
With a wicked heart he deviseth evil, and at all times he soweth discord.
15 Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
To such a one his destruction shall presently come, and he shall suddenly be destroyed, and shall no longer have any remedy.
16 Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
Six things there are, which the Lord hateth, and the seventh his soul detesteth:
17 duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
Haughty eyes, a lying tongue, hands that shed innocent blood,
18 zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
A heart that deviseth wicked plots, feet that are swift to run into mischief,
19 mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
A deceitful witness that uttereth lies, and him that soweth discord among brethren.
20 Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
My son, beep the commandments of thy father, and forsake not the law of thy mother.
21 Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
Bind them in thy heart continually, and put them about thy neck.
22 Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
When thou walkest, let them go with thee: when thou sleepest, let them keep thee; and when thou awakest, talk with them.
23 Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
Because the commandment is a lamp, and the law a light, and reproofs of instruction are the way of life:
24 suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
That they may keep thee from the evil woman, and from the flattering tongue of the stranger.
25 Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
Let not thy heart covet her beauty, be not caught with her winks:
26 Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
For the price of a harlot is scarce one loaf: but the woman catcheth the precious soul of a man.
27 Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
Can a man hide fire in his bosom, and his garments not burn?
28 Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
Or can he walk upon hot coals, and his feet not be burnt?
29 Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
So he that goeth in to his neighbour’s wife, shall not be clean when he shall touch her.
30 Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
The fault is not so great when a man hath stolen: for he stealeth to fill his hungry soul:
31 Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
And if he be taken he shall restore sevenfold, and shall give up all the substance of his house.
32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
But he that is an adulterer, for the folly of his heart shall destroy his own soul:
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
He gathereth to himself shame and dishonour, and his reproach shall not be blotted out:
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
Because the jealousy and rage of the husband will not spare in the day of revenge,
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.
Nor will he yield to any man’s prayers, nor will he accept for satisfaction ever so many gifts.

< Karin Magana 6 >