< Karin Magana 5 >
1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
Filho meu, presta atenção à minha sabedoria, inclina teus ouvidos ao meu entendimento.
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
Para que guardes o bom-senso; e teus lábios conservem o conhecimento.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
Porque os lábios da mulher pervertida gotejam mel; e sua boca é mais suave que o azeite.
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
Porém seu fim é mais amargo que o absinto; é afiado como a espada de dois fios.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
Seus pés descem à morte; seus passos conduzem ao Xeol. (Sheol )
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
Para que não ponderes a vereda da vida, os percursos delas são errantes, e tu não os conhecerás.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
E agora, filhos, escutai-me; e não vos desvieis das palavras de minha boca.
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Mantenha teu caminho longe dela; e não te aproximes da porta da casa dela.
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
Para que não dês tua honra a outros, nem teus anos [de vida] aos cruéis.
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
Para que estranhos não se fartem de teu poder, e teus trabalhos [não sejam] aproveitados em casa alheia;
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
E gemas em teu fim, quando tua carne e teu corpo estiverem consumidos.
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
E digas: Como eu odiei a correção, e meu coração desprezou a repreensão?
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
E não escutei a voz de meus ensinadores, nem ouvi a meus mestres.
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
Quase me achei em todo mal, no meio da congregação e do ajuntamento.
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Bebe água de tua [própria] cisterna, e das correntes de teu [próprio] poço.
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
Derramar-se-iam por fora tuas fontes, [e] pelas ruas os ribeiros de águas?
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
Sejam somente para ti, e não para os estranhos contigo.
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Seja bendito o teu manancial, e alegra-te com a mulher de tua juventude.
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
[Seja ela] uma cerva amorosa e gazela graciosa; que os seios dela te fartem em todo tempo; e anda pelo caminho do amor dela continuamente.
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
E por que tu, filho meu, andarias perdido pela estranha, e abraçarias o peito da [mulher] alheia?
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
Pois os caminhos do homem estão perante os olhos do SENHOR; e ele pondera todos os seus percursos.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
O perverso será preso pelas suas [próprias] perversidades; e será detido pelas cordas de seu [próprio] pecado.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
Ele morrerá pela falta de correção; e andará sem rumo pela grandeza de sua loucura.