< Karin Magana 5 >

1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
Mein Sohn, merke auf meine Weisheit und leihe meiner Einsicht dein Ohr,
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
um Besonnenheit zu beobachten und damit deine Lippen Erkenntnis bewahren.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
Denn von Honigseim triefen die Lippen der fremden Frau, und glätter als Öl ist ihr Gaumen;
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
aber zuletzt ist sie bitter wie Wermut, scharf wie ein zweischneidiges Schwert.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
Ihre Füße steigen zum Tode hinab, ihre Schritte sind geradeswegs zur Unterwelt gerichtet. (Sheol h7585)
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
Damit du nicht den Weg des Lebens einschlägst, sind ihre Bahnen unstet, ohne daß du es merkst.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Nun denn, mein Sohn, höre auf mich und weiche nicht ab von den Worten meines Mundes!
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Halte deinen Weg fern von ihr und nahe dich nicht der Tür ihres Hauses,
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
damit du nicht anderen deine Ehre hingeben mußt und (den Ertrag) deiner Jahre einem unerbittlichen (Rächer);
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
damit nicht Fremde sich an deinem Vermögen sättigen und dein mühsam Erworbenes nicht in das Haus eines andern kommt,
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
und du nicht schließlich seufzen mußt, wenn dir Leib und Fleisch dahingeschwunden ist,
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
und du klagen mußt: »Ach, warum habe ich die Zucht gehaßt, und warum hat mein Herz die Warnung mißachtet!
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
Warum habe ich nicht auf die Stimme meiner Lehrer gehört und meinen Erziehern kein Gehör geschenkt!
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
Beinahe wäre ich ganz ins Verderben geraten inmitten der Gerichtsversammlung und in der Gemeinde!«
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Trinke Wasser nur aus deiner eigenen Zisterne und Quellwasser aus deinem eigenen Born!
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
Sollen deine Quellen sich auf die Straße ergießen, deine Wasserbäche auf die freien Plätze?
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
Nein, dir allein sollen sie angehören und keinem Fremden neben dir.
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Dein Brunnquell möge gesegnet sein, daß du am Weibe deiner Jugend dich erfreust!
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
Das liebreizende Reh, die anmutige Gazelle – ihr Busen möge dich allezeit ergötzen, in ihrer Liebe sei immerdar trunken!
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
Denn warum wolltest du, mein Sohn, an einer Fremden dich ergötzen und den Busen einer anderen umarmen? –
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
Denn vor den Augen des HERRN liegen die Wege eines jeden offen da, und auf alle seine Pfade gibt er acht.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
Die eigenen Verschuldungen fangen ihn, den Gottlosen, und durch die Bande seiner Sünde wird er festgehalten.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
Sterben wird ein solcher infolge des Mangels an Zucht und ob seiner großen Torheit zum Sturz hintaumeln.

< Karin Magana 5 >