< Karin Magana 5 >
1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
Mein Sohn, merke auf meine Weisheit, neige dein Ohr zu meiner Einsicht,
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
um Besonnenheit zu beobachten, und damit deine Lippen Erkenntnis bewahren.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
Denn Honigseim träufeln die Lippen der Fremden, und glatter als Öl ist ihr Gaumen;
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
aber ihr Letztes ist bitter wie Wermut, scharf wie ein zweischneidiges Schwert.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
Ihre Füße steigen hinab zum Tode, an dem Scheol haften ihre Schritte. (Sheol )
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
Damit sie nicht den Weg des Lebens einschlage, schweifen ihre Bahnen, ohne daß sie es weiß.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Nun denn, ihr Söhne, höret auf mich, und weichet nicht ab von den Worten meines Mundes!
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Halte fern von ihr deinen Weg, und nahe nicht zu der Tür ihres Hauses:
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
damit du nicht anderen deine Blüte gebest, und deine Jahre dem Grausamen;
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
damit nicht Fremde sich sättigen an deinem Vermögen, und dein mühsam Erworbenes nicht komme in eines Ausländers Haus;
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
und du nicht stöhnest bei deinem Ende, wenn dein Fleisch und dein Leib dahinschwinden, und sagest:
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
Wie habe ich die Unterweisung gehaßt, und mein Herz hat die Zucht verschmäht!
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
Und ich habe nicht gehört auf die Stimme meiner Unterweiser, und mein Ohr nicht zugeneigt meinen Lehrern.
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
Wenig fehlte, so wäre ich in allem Bösen gewesen, inmitten der Versammlung und der Gemeinde.
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Trinke Wasser aus deiner Zisterne und Fließendes aus deinem Brunnen.
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
Mögen nach außen sich ergießen deine Quellen, deine Wasserbäche auf die Straßen.
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
Dir allein sollen sie gehören, und nicht Fremden mit dir.
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Deine Quelle sei gesegnet, und erfreue dich an dem Weibe deiner Jugend;
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
die liebliche Hindin und anmutige Gemse, ihre Brüste mögen dich berauschen zu aller Zeit, taumle stets in ihrer Liebe.
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
Und warum solltest du, mein Sohn, an einer Fremden taumeln, und den Busen einer Fremden umarmen? -
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
Denn vor den Augen Jehovas sind eines jeden Wege, und alle seine Geleise wägt er ab.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
Die eigenen Missetaten werden ihn, den Gesetzlosen, fangen, und in seiner Sünde Banden wird er festgehalten werden.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
Sterben wird er, weil ihm Zucht mangelt, und in der Größe seiner Torheit wird er dahintaumeln.