< Karin Magana 5 >

1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
My son, attend to my wisdom. And bow thine ear to my understanding;
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
That thou mayest keep discretion, And that thy lips may preserve knowledge!
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
Truly, the lips of a strange woman drop honey, And her mouth is smoother than oil;
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
But her end is bitter as wormwood, Sharp as a two-edged sword.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
Her feet go down to death; Her steps lay hold of the under-world. (Sheol h7585)
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
That she may not ponder the way of life, Her paths waver when she heedeth it not.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Hear me now, therefore, O children! And turn not away from the words of my mouth!
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Remove thy way far from her. And come not nigh the door of her house:
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
Lest thou give thy bloom to others, And thy years to a cruel one;
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
Lest strangers be filled with thy wealth, And thine earnings be in the house of an alien;
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
And lest thou mourn in thy latter end. When thy flesh and thy body are consumed,
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
And say, “How have I hated instruction! And how hath my heart despised reproof!
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
I have not obeyed the voice of my teachers, Nor inclined mine ear to my instructors;
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
I have well-nigh fallen into utter misery; In the midst of the congregation and the assembly.”
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Drink water out of thine own cistern. And running water out of thine own well:
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
So shall thy fountains overflow in the streets, In the wide streets, as streams of water;
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
They shall belong to thee alone, And not to strangers with thee;
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
And thy fountain shall be blessed, Yea, thou shalt have joy in the wife of thy youth.
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
A lovely hind, a graceful doe, Her breasts shall satisfy thee at all times, And thou shalt be always ravished with her love.
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
Why, then, my son, wilt thou be ravished with a wanton, And embrace the bosom of a stranger?
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
For the ways of man are before the eyes of the LORD, And he weigheth well all his paths.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
His own iniquities shall ensnare the wicked; Yea, he shall be held fast by the cords of his own sins.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
He shall die for want of instruction; Yea, through the greatness of his folly he shall stagger.

< Karin Magana 5 >