< Karin Magana 5 >
1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
My sonne, hearken vnto my wisedome, and incline thine eare vnto my knowledge.
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
That thou maiest regarde counsell, and thy lippes obserue knowledge.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
For the lippes of a strange woman drop as an honie combe, and her mouth is more soft then oyle.
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
But the end of her is bitter as wormewood, and sharpe as a two edged sworde.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
Her feete goe downe to death, and her steps take holde on hell. (Sheol )
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
She weigheth not the way of life: her paths are moueable: thou canst not knowe them.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Heare yee me nowe therefore, O children, and depart not from the wordes of my mouth.
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Keepe thy way farre from her, and come not neere the doore of her house,
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
Least thou giue thine honor vnto others, and thy yeeres to the cruell:
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
Least the stranger should be silled with thy strength, and thy labours bee in the house of a stranger,
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
And thou mourne at thine end, (when thou hast consumed thy flesh and thy bodie)
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
And say, How haue I hated instruction, and mine heart despised correction!
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
And haue not obeied the voyce of them that taught mee, nor enclined mine eare to them that instructed me!
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
I was almost brought into all euil in ye mids of the Congregation and assemblie.
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Drinke the water of thy cisterne, and of the riuers out of the middes of thine owne well.
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
Let thy fountaines flow foorth, and the riuers of waters in the streetes.
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
But let them bee thine, euen thine onely, and not the strangers with thee.
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Let thy fountaine be blessed, and reioyce with the wife of thy youth.
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
Let her be as the louing hinde and pleasant roe: let her brests satisfie thee at all times, and delite in her loue continually.
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
For why shouldest thou delite, my sonne, in a strange woman, or embrace the bosome of a stranger?
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
For the waies of man are before the eyes of the Lord, and he pondereth all his pathes.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
His owne iniquities shall take the wicked himselfe, and he shall be holden with the cordes of his owne sinne.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
Hee shall die for fault of instruction, and shall goe astray through his great follie.