< Karin Magana 5 >

1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
Mærk dig, min Søn, min Visdom, bøj til min Indsigt dit Øre,
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
at Kløgt maa vaage øver dig, Læbernes Kundskab vare paa dig.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
Thi af Honning drypper den fremmedes Læber, glattere end Olie er hendes Gane;
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
men til sidst er hun besk som Malurt, hvas som tveægget Sværd;
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
hendes Fødder styrer nedad mod Døden, til Dødsriget stunder hendes Fjed; (Sheol h7585)
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
hun følger ej Livets Vej, hendes Spor er bugtet, hun ved det ikke.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Hør mig da nu, min Søn, vig ikke fra min Munds Ord!
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Lad din Vej være langt fra hende, kom ej hendes Husdør nær,
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
at du ikke maa give andre din Ære, en grusom Mand dine Aar.
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
at ikke dit Gods skal mætte fremmede, din Vinding ende i Andenmands Hus,
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
saa du gribes af Anger til sidst, naar dit Kød og Huld svinder hen,
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
og du siger: »Ak, at jeg hadede Tugt, at mit Hjerte lod haant om Revselse,
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
saa jeg ikke lød mine Læreres Røst, ej bøjed mit Øre til dem, som lærte mig!
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
Nær var jeg kommet i alskens Ulykke midt i Forsamling og Menighed!«
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Drik Vand af din egen Cisterne og rindende Vand af din Brønd;
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
lad ej dine Kilder flyde paa Gaden, ej dine Bække paa Torvene!
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
Dig skal de tilhøre, dig alene, ingen fremmed ved Siden af dig!
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Velsignet være dit Væld, og glæd dig ved din Ungdoms Hustru,
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
den elskelige Hind, den yndige Gazel; hendes Elskov fryde dig stedse, berus dig altid i hendes Kærlighed!
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
Hvi beruser du dig, min Søn, i en fremmed og tager en andens Hustru i Favn?
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
Thi for HERRENS Øjne er Menneskets Veje, grant følger han alle dets Spor;
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
den gudløse fanges af egen Brøde og holdes fast i Syndens Reb;
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
han dør af Mangel paa Tugt, gaar til ved sin store Daarskab.

< Karin Magana 5 >