< Karin Magana 31 >
1 Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
Palabras de Lemuel rey: la profecía con que le enseñó su madre.
2 “Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
¿Qué, hijo mío? ¿Y qué, hijo de mi vientre? ¿y qué, hijo de mis deseos?
3 Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
No des a las mujeres tu fuerza, ni tus caminos, que es para destruir a los reyes.
4 “Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
No es de los reyes, o! Lemuel, no es de los reyes beber vino, ni de los príncipes la cerveza:
5 don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
Porque no beban, y olviden la ley; y perviertan el derecho de todos los hijos afligidos.
6 A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
Dad la cerveza al que perece, y el vino a los de amargo ánimo.
7 bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
Beban, y olvídense de su necesidad, y de su miseria no se acuerden más.
8 “Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
Abre tu boca por el mudo, en el juicio de todos los hijos de muerte.
9 Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
Abre tu boca, juzga justicia, y el derecho del pobre, y del menesteroso.
10 Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
¿Mujer valiente quién la hallará? porque su valor luengamente pasa al de las piedras preciosas.
11 Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
El corazón de su marido está en ella confiado, y de despojo no tendrá necesidad.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
Dárle ha bien, y no mal, todos los días de su vida.
13 Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
Buscó lana y lino; y de voluntad trabajó con sus manos.
14 Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
Fue como navío de mercader, que trae su pan de lejos.
15 Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
Levantóse aun de noche; y dio comida a su familia; y ración a sus criadas.
16 Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
Consideró la heredad, y compróla; y plantó viña del fruto de sus manos.
17 Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
Ciñó sus lomos de fortaleza, y esforzó sus brazos.
18 Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
Gustó que era buena su granjería; su candela no se apagó de noche.
19 Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
Aplicó sus manos al huso; y sus manos trataron la rueca.
20 Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
Su mano extendió al pobre; y al menesteroso extendió sus manos.
21 Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
No tendrá temor de la nieve por su familia, porque toda su familia está vestida de ropas dobladas.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
Ella se hizo tapices: de lino fino y púrpura es su vestido.
23 Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
Conocido es su marido en las puertas, cuando se asienta con los ancianos de la tierra.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
Hizo telas, y vendió; y dio cintas al mercader.
25 Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
Fortaleza y hermosura es su vestido; y en el día postrero reirá.
26 Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
Abrió su boca con sabiduría; y la ley de clemencia está en su boca.
27 Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
Considera los caminos de su casa; y no comió el pan de balde.
28 ’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
Levantáronse sus hijos, y llamáronla bienaventurada; y su marido también la alabó.
29 “Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
Muchas mujeres hicieron riquezas, mas tú las sobrepujaste a todas.
30 Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
Engañosa es la gracia, y vana la hermosura: la mujer que teme a Jehová, esa será alabada.
31 Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
Dádla del fruto de sus manos; y alábenla en las puertas sus hechos.