< Karin Magana 31 >
1 Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
Amazwi enkosi uLemuweli, amazwi enhlakanipho awafundiswa ngunina:
2 “Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
Oh, ndodana yami! Oh ndodana yethumbu lami! Oh, ndodana yezifungo zami,
3 Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
ungadlalisi amandla akho ebafazini, izifutho zakho kulabo abadiliza amakhosi.
4 “Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
Kakusikho kwamakhosi, bakithi Lemuweli kakusikho kwamakhosi ukunatha iwayini, kakusikho kwababusi ukunxwanela utshwala,
5 don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
funa badakwe bakhohlwe izimiso zomthetho, behluleke ukumisela kuhle abahluphekayo amalungelo abo.
6 A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
Phana utshwala kulabo abavele sebezifele, iwayini kulabo abalosizi olukhulu;
7 bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
kabanathe bakhohlwe ubuyanga babo bakhohlwe nya usizi lwabo.
8 “Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
Bamele labo abehlulekayo ukuzikhulumela, uwamele amalungelo alabo abangelalutho.
9 Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
Khuluma njalo wahlulele ngokulunga; alwele amalungelo abayanga labaswelayo.
10 Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
Ngubani na ongathola umfazi olesimilo? Uligugu elidlula kakhulu amatshe amahle.
11 Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
Indoda yakhe iyamthemba ngokupheleleyo njalo kayisweli lutho oluqakathekileyo.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
Uyenzela okuhle, hatshi okubi, empilweni yakhe yonke.
13 Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
Uyakhetha kuhle iwulu lesikusha akweluke kuhle ngezandla ezikhutheleyo.
14 Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
Unjengemikhumbi yabathengisi, eletha ukudla okuvela kude.
15 Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
Uvuka ekuseni kusesemnyama; alungisele abomuzi wakhe ukudla abele lezincekukazi zakhe.
16 Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
Uyayihlolisisa insimu mandulo kokuyithenga; ngalokho akuzuzayo uyahlanyela isivini sakhe.
17 Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
Uwubamba ngokukhuthala umsebenzi wakhe; aqinise izingalo zakhe emsebenzini.
18 Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
Uyananzelela ukuthi ukuthengisa kwakhe kulenzuzo, lokuthi isibane sakhe kasicimi ebusuku.
19 Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
Uphatha uluthi lokuphotha ngesandla sakhe abesebamba ngeminwe yakhe isigudugudu sokweluka.
20 Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
Welulela izandla zakhe kubayanga njalo ulezandla ezilula kwabaswelayo.
21 Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
Lapho kukhithika ungqwaqwane, kalakwesaba ngabendlu yakhe; ngoba bonke bagqoke ezibomvu.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
Wendlala amalembu ombheda wakhe; agqoke ilineni elihle lezigqoko eziyibubende.
23 Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
Indoda yakhe iyahlonitshwa enkundleni lapho efika ihlale khona ndawonye labadala belizwe.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
Uthunga izigqoko zelineni azithengise, abathengi bemigaxo bayizuza kuye.
25 Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
Wembethe amandla lesithunzi; uyahleka loba kusiza insuku ezimbi.
26 Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
Ukhuluma ngenhlakanipho, lezeluleko eziqondileyo zisolimini lwakhe.
27 Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
Unqinekela ezomuzi wakhe njalo kadli isinkwa sobuvila.
28 ’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
Abantwabakhe bayambonga bathi ubusisiwe; lendoda yakhe layo iyamdumisa ithi,
29 “Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
“Banengi abafazi abenza izimangaliso zobuhle, kodwa wena uyabedlula bonke.”
30 Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
Ukubukeka kuyakhohlisa, lobuhle buyaphela; kodwa umfazi owesaba uThixo kadunyiswe.
31 Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
Kaphiwe umvuzo wobuhle abenzayo, imisebenzi yakhe imlethele udumo enkundleni.