< Karin Magana 31 >

1 Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
The words of king Lemuel, the prophecy that his mother taught him.
2 “Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
What, my son? and what, the son of my womb? and what, the son of my vows?
3 Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
Give not thy strength to women, nor thy ways to that which destroyeth kings.
4 “Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
[It is] not for kings, O Lemuel, [it is] not for kings to drink wine; nor for princes strong drink:
5 don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
Lest they drink, and forget the law, and pervert the judgment of any of the afflicted.
6 A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
Give strong drink to him that is ready to perish, and wine to those that are of heavy hearts.
7 bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
Let him drink, and forget his poverty, and remember his misery no more.
8 “Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
Open thy mouth for the dumb in the cause of all such as are appointed to destruction.
9 Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
Open thy mouth, judge righteously, and plead the cause of the poor and needy.
10 Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
Who can find a virtuous woman? for her price [is] far above rubies.
11 Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
The heart of her husband doth safely trust in her, so that he shall have no need of spoil.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
She will do him good and not evil all the days of her life.
13 Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
She seeketh wool, and flax, and worketh willingly with her hands.
14 Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
She is like the merchant's ships; she bringeth her food from afar.
15 Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
She riseth also while it is yet night, and giveth food to her household, and a portion to her maidens.
16 Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
She considereth a field, and buyeth it: with the fruit of her hands she planteth a vineyard.
17 Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
She girdeth her loins with strength, and strengtheneth her arms.
18 Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
She perceiveth that her merchandise [is] good: her candle goeth not out by night.
19 Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
She layeth her hands to the spindle, and her hands hold the distaff.
20 Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
She stretcheth out her hand to the poor; yes, she reacheth forth her hands to the needy.
21 Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
She is not afraid of the snow for her household: for all her household [are] clothed with scarlet.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
She maketh herself coverings of tapestry; her clothing [is] silk and purple.
23 Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
Her husband is known in the gates, when he sitteth among the elders of the land.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
She maketh fine linen, and selleth [it]; and delivereth girdles to the merchant.
25 Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
Strength and honor [are] her clothing; and she shall rejoice in time to come.
26 Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
She openeth her mouth with wisdom; and on her tongue [is] the law of kindness.
27 Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
She looketh well to the ways of her household, and eateth not the bread of idleness.
28 ’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
Her children rise up, and call her blessed; her husband [also], and he praiseth her.
29 “Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
Many daughters have done virtuously, but thou excellest them all.
30 Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
Favor [is] deceitful, and beauty [is] vain: [but] a woman [that] feareth the LORD, she shall be praised.
31 Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
Give her of the fruit of her hands; and let her own works praise her in the gates.

< Karin Magana 31 >