< Karin Magana 31 >
1 Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
The words of king Lamuel. The vision wherewith his mother instructed him.
2 “Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
What, O my beloved, what, O the beloved of my womb, what, O the beloved of my vows?
3 Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
Give not thy substance to women, and thy riches to destroy kings.
4 “Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
Give not to kings, O Lamuel, give not wine to kings: because there is no secret where drunkenness reigneth:
5 don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
And lest they drink and forget judgments, and pervert the cause of the children of the poor.
6 A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
Give strong drink to them that are sad: and wine to them that are grieved in mind:
7 bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
Let them drink, and forget their want, and remember their sorrow no more.
8 “Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
Open thy mouth for the dumb, and for the causes of all the children that pass.
9 Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
Open thy mouth, decree that which is just, and do justice to the needy and poor.
10 Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
Who shall find a valiant woman? far and from the uttermost coasts is the price of her.
11 Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
The heart of her husband trusteth in her, and he shall have no need of spoils.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
She will render him good, and not evil, all the days of her life.
13 Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
She hath sought wool and flax, and hath wrought by the counsel of her hands.
14 Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
She is like the merchant’s ship, she bringeth her bread from afar.
15 Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
And she hath risen in the night, and given a prey to her household, and victuals to her maidens.
16 Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
She hath considered a field, and bought it: with the fruit of her hands she hath planted a vineyard.
17 Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
She hath girded her loins with strength, and hath strengthened her arm.
18 Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
She hath tasted and seen that her traffic is good: her lamp shall not be put out in the night.
19 Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
She hath put out her hand to strong things, and her fingers have taken hold of the spindle.
20 Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
She hath opened her hand to the needy, and stretched out her hands to the poor.
21 Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
She shall not fear for her house in the cold of snow: for all her domestics are clothed with double garments.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
She hath made for herself clothing of tapestry: fine linen, and purple is her covering.
23 Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
Her husband is honourable in the gates, when he sitteth among the senators of the land.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
She made fine linen, and sold it, and delivered a girdle to the Chanaanite.
25 Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
Strength and beauty are her clothing, and she shall laugh in the latter day.
26 Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
She hath opened her mouth to wisdom, and the law of clemency is on her tongue.
27 Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
She hath looked well to the paths of her house, and hath not eaten her bread idle.
28 ’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
Her children rose up, and called her blessed: her husband, and he praised her.
29 “Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
Many daughters have gathered together riches: thou hast surpassed them all.
30 Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
Favour is deceitful, and beauty is vain: the woman that feareth the Lord, she shall be praised.
31 Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
Give her of the fruit of her hands: and let her works praise her in the gates.