< Karin Magana 30 >
1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Detta är Agurs, Jakes sons, ord och utsaga. Så talade den mannen till Itiel -- till Itiel och Ukal.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Ja, jag är för oförnuftig för att kunna räknas såsom människa, jag har icke mänskligt förstånd;
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
vishet har jag icke fått lära, så att jag äger kunskap om den Helige.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Vem har stigit upp till himmelen och åter farit ned? Vem har samlat vinden i sina händer? Vem har knutit in vattnet i ett kläde? Vem har fastställt jordens alla gränser? Vad heter han, och vad heter hans son -- du vet ju det?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Allt Guds tal är luttrat; han är en sköld för dem som taga sin tillflykt till honom.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Lägg icke något till hans ord, på det att han icke må beslå dig med lögn.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Om två ting beder jag dig, vägra mig dem icke, intill min död:
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Låt fåfänglighet och lögn vara fjärran ifrån mig; och giv mig icke fattigdom, ej heller rikedom, men låt mig få det bröd mig tillkommer.
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
Jag kunde eljest, om jag bleve alltför matt, förneka dig, att jag sporde: "Vem är HERREN?" eller om jag bleve alltför fattig, kunde jag bliva en tjuv, ja, förgripa mig på min Guds namn.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Förtala icke en tjänare inför hans herre; han kunde eljest förbanna dig, så att du stode där med skam.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
Ett släkte där man förbannar sin fader, och där man icke välsignar sin moder;
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
ett släkte som tycker sig vara rent, fastän det icke har avtvått sin orenlighet;
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
ett släkte -- huru stolta äro icke dess ögon, och huru fulla av högmod äro icke dess blickar!
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
ett släkte vars tänder äro svärd, och vars kindtänder äro knivar, så att de äta ut de betryckta ur landet och de fattiga ur människornas krets!
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Blodigeln har två döttrar: "Giv hit, giv hit." Tre finnas, som icke kunna mättas, ja, fyra, som aldrig säga: "Det är nog":
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol )
dödsriket och den ofruktsammas kved, jorden, som icke kan mättas med vatten, och elden, som aldrig säger: "Det är nog." (Sheol )
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Den som bespottar sin fader och försmår att lyda sin moder hans öga skola korparna vid bäcken hacka ut, och örnens ungar skola äta upp det.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Tre ting äro mig för underbara, ja, fyra finnas, som jag icke kan spåra:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
örnens väg under himmelen, ormens väg över klippan, skeppets väg mitt i havet och en mans väg hos en ung kvinna.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Sådant är äktenskapsbryterskans sätt: hon njuter sig mätt och stryker sig så om munnen och säger: "Jag har intet orätt gjort."
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Tre finnas, under vilka jorden darrar, ja, fyra, under vilka den ej kan uthärda:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
under en träl, när han bliver konung, och en dåre, när han får äta sig mätt,
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
under en försmådd kvinna, när hon får man och en tjänstekvinna, när hon tränger undan sin fru.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Fyra finnas, som äro små på jorden, och likväl är stor vishet dem beskärd:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
myrorna äro ett svagt folk, men de bereda om sommaren sin föda;
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
klippdassarna äro ett folk med ringa kraft, men i klippan bygga de sig hus;
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
gräshopporna hava ingen konung, men i härordning draga de alla ut;
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
gecko-ödlan kan gripas med händerna, dock bor hon i konungapalatser.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Tre finnas, som skrida ståtligt fram, ja, fyra, som hava en ståtlig gång:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
lejonet, hjälten bland djuren, som ej viker tillbaka för någon,
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
en stridsrustad häst och en bock och en konung i spetsen för sin här.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Om du har förhävt dig, evad det var dårskap eller det var medveten synd, så lägg handen på munnen.
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
Ty såsom ost pressas ut ur mjölk, och såsom blod pressas ut ur näsan, så utpressas kiv ur vrede. ----