< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
verba Congregantis filii Vomentis visio quam locutus est vir cum quo est Deus et qui Deo secum morante confortatus ait
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
stultissimus sum virorum et sapientia hominum non est mecum
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
non didici sapientiam et non novi sanctorum scientiam
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
quis ascendit in caelum atque descendit quis continuit spiritum manibus suis quis conligavit aquas quasi in vestimento quis suscitavit omnes terminos terrae quod nomen eius et quod nomen filii eius si nosti
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
omnis sermo Dei ignitus clypeus est sperantibus in se
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
ne addas quicquam verbis illius et arguaris inveniarisque mendax
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
duo rogavi te ne deneges mihi antequam moriar
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
vanitatem et verba mendacia longe fac a me mendicitatem et divitias ne dederis mihi tribue tantum victui meo necessaria
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
ne forte saturatus inliciar ad negandum et dicam quis est Dominus et egestate conpulsus furer et peierem nomen Dei mei
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
ne accuses servum ad dominum suum ne forte maledicat tibi et corruas
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
generatio quae patri suo maledicit et quae non benedicit matri suae
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
generatio quae sibi munda videtur et tamen non est lota a sordibus suis
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
generatio cuius excelsi sunt oculi et palpebrae eius in alta subrectae
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
generatio quae pro dentibus gladios habet et commandit molaribus suis ut comedat inopes de terra et pauperes ex hominibus
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
sanguisugae duae sunt filiae dicentes adfer adfer tria sunt insaturabilia et quartum quod numquam dicit sufficit
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
infernus et os vulvae et terra quae non satiatur aqua ignis vero numquam dicit sufficit (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
oculum qui subsannat patrem et qui despicit partum matris suae effodiant corvi de torrentibus et comedant illum filii aquilae
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
tria sunt difficilia mihi et quartum penitus ignoro
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
viam aquilae in caelo viam colubri super petram viam navis in medio mari et viam viri in adulescentula
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
talis est via mulieris adulterae quae comedit et tergens os suum dicit non sum operata malum
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
per tria movetur terra et quartum non potest sustinere
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
per servum cum regnaverit per stultum cum saturatus fuerit cibo
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
per odiosam mulierem cum in matrimonio fuerit adsumpta et per ancillam cum heres fuerit dominae suae
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
quattuor sunt minima terrae et ipsa sunt sapientiora sapientibus
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
formicae populus infirmus quae praeparant in messe cibum sibi
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
lepusculus plebs invalida quae conlocat in petra cubile suum
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
regem lucusta non habet et egreditur universa per turmas
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
stilio manibus nititur et moratur in aedibus regis
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
tria sunt quae bene gradiuntur et quartum quod incedit feliciter
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
leo fortissimus bestiarum ad nullius pavebit occursum
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
gallus succinctus lumbos et aries nec est rex qui resistat ei
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
et qui stultus apparuit postquam elatus est in sublime si enim intellexisset ori inposuisset manum
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
qui autem fortiter premit ubera ad eliciendum lac exprimit butyrum et qui vehementer emungitur elicit sanguinem et qui provocat iras producit discordias

< Karin Magana 30 >