< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Inilah perkataan Agur anak Yake, suatu perkataan bijak. Tuhan, aku lelah dan kehabisan tenaga.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Sungguh aku ini manusia yang paling bodoh dan tidak berakal budi.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
Kebijaksanaan tidak aku kuasai, sehingga aku tak dapat mengenal Yang Mahakudus.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Tetapi tidak seorang pun lebih berpengalaman daripadaku, sehingga dapat mengenal Dia yang pernah naik ke surga lalu turun kembali, Dia yang pernah menggenggam angin dalam tangannya, Dia yang pernah membungkus air dalam kain, dan Dia yang menetapkan batas-batas bumi. Kalau engkau begitu hebat, beritahukanlah kepadaku nama-Nya dan nama Anak-Nya!
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Semua firman Allah terbukti benar. Dia seperti perisai bagi orang yang berlindung pada-Nya.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Jangan menambahi apa pun kepada firman-Nya, karena Dia akan menegurmu dan engkau ketahuan menipu.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Ya TUHAN, kabulkanlah dua permintaanku ini sebelum aku mati:
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Pertama, tolonglah aku untuk hidup dengan jujur. Kedua, janganlah memberiku kekayaan atau kemiskinan, tetapi berikanlah hanya makanan yang aku butuhkan.
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
Karena bila aku kaya, mungkin aku menjadi sombong dan berkata “Aku tidak perlu TUHAN.” Tetapi apabila aku, sebagai hamba-Mu, jatuh miskin dan mencuri sesuatu, maka nama-Mu, ya Allahku, akan ikut dicemarkan.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Jangan menjelekkan seorang budak kepada tuannya. Jika budak itu tahu, dia akan memfitnahmu, dan engkau akan menanggung akibatnya.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
Ada jenis orang yang mengutuk ayah mereka dan tidak menghargai ibu mereka.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
Ada jenis orang yang merasa diri mereka suci, tetapi kenyataannya mereka kotor dan najis.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
Ada jenis orang yang menunjukkan kesombongan dan memandang rendah orang lain.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
Ada jenis orang yang rakus dan kejam bagai hewan buas bergigi tajam. Mereka memangsa orang-orang miskin dan lemah hingga lenyap dari antara manusia di muka bumi.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Manusia serakah bagaikan lintah yang tak pernah puas mengisap darah. Dia hanya memikirkan diri sendiri dan berkata, “Untukku dan untukku!” Ada beberapa hal yang tidak akan pernah bisa penuh atau merasa puas:
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
Syeol, wanita yang tidak pernah melahirkan anak, tanah kering yang tak pernah cukup menyerap air, dan api yang tak akan berhenti membakar apa pun di dekatnya. (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Bila engkau memandang rendah ayahmu dan menolak taat kepada ibumu, burung gagak akan mematuk matamu dan anak rajawali memakan tubuhmu.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Ada beberapa hal yang masih menjadi rahasia— hal-hal yang tidak aku mengerti:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
Bagaimana caranya elang terbang di udara, cara ular menjalar di batu-batu, bagaimana nahkoda kapal mengetahui jalurnya di tengah laut, dan bagaimana terbentuknya perasaan pemuda kepada seorang gadis.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Hal yang juga mengherankan adalah seorang pezina yang tidak merasa bersalah setelah berbuat dosa. Dengan entengnya dia membersihkan diri lalu berkata, “Aku tidak bersalah,” seakan dia hanya makan lalu membasuh mulut.
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Ada beberapa hal yang membuat bumi bergoncang dan gempar:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
Seorang budak yang tiba-tiba menjadi raja, orang bebal yang mendapatkan segala keinginannya,
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
wanita yang menyebalkan tetapi mendapat suami, dan budak perempuan yang menggantikan posisi istri tuannya.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Di bumi ini, ada empat binatang yang kecil tetapi sangat bijaksana:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
Semut: Bukan hewan yang kuat, tetapi mengangkut makanan pada musim panas.
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
Tikus gunung: Binatang yang lemah, tetapi membuat sarang di pegunungan.
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
Belalang: Tidak memiliki pemimpin tetapi mereka terbang berkelompok dengan teratur seperti barisan pasukan tempur.
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
Cicak: Bisa ditangkap dengan tangan, tetapi ada di istana-istana para raja.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Ada beberapa makhluk hidup yang berjalan dengan gagah:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
Singa, yang paling kuat di antara hewan lain dan tidak mundur dari ancaman apa pun.
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
Ayam jantan dan kambing jantan berjalan dengan gagah, juga raja ketika memimpin pasukannya.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Bila engkau sudah bertindak bodoh dengan menyombongkan diri atau merencanakan hal jahat, bekaplah mulutmu dan diamlah saja!
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
Seperti memeras kelapa akan menghasilkan santan dan meremas hidung akan mengeluarkan darah, demikianlah memeras amarah akan menghasilkan pertengkaran.

< Karin Magana 30 >