< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Paroles d’Agur, fils de Jaké; sentence. Cet homme a dit: Je me suis fatigué pour connaître Dieu, pour connaître Dieu, et je suis à bout de forces.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Car je suis plus stupide que personne, et je n’ai pas l’intelligence d’un homme.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
Je n’ai pas appris la sagesse, et je ne connais pas la science du Saint.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Qui monte au ciel et qui en descend? Qui a recueilli le vent dans ses mains? Qui a lié les eaux dans son vêtement? Qui a affermi toutes les extrémités de la terre? Quel est son nom et quel est le nom de son fils? Le sais-tu?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Toute parole de Dieu est éprouvée par le feu; il est un bouclier pour ceux qui se réfugient auprès de lui.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
N’ajoute rien à ses paroles, de peur qu’il ne te reprenne et que tu ne sois trouvé menteur.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Je te demande deux choses, ne me les refuse pas avant que je meure:
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Eloigne de moi la fausseté et la parole mensongère; ne me donne ni pauvreté, ni richesse, accorde-moi le pain qui m’est nécessaire:
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
de peur que, rassasié, je ne te renie et ne dise: « Qui est Yahweh? »; et que, devenu pauvre, je ne dérobe, et n’outrage le nom de mon Dieu.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Ne calomnie pas un serviteur auprès de son maître, de peur qu’il ne te maudisse et que tu n’en portes la peine.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
Il est une race qui maudit son père, et qui ne bénit pas sa mère.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
Il est une race qui est pure à ses propres yeux, et qui n’est pas lavée de sa souillure.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
Il est une race — combien ses regards sont altiers, et ses paupières élevées!
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
Il est une race dont les dents sont des glaives, et les molaires des couteaux, pour dévorer les malheureux de dessus la terre, et les indigents parmi les hommes.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
La sangsue a deux filles: Donne! donne! Trois choses sont insatiables, quatre ne disent jamais: Assez:
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
le schéol, le sein stérile, la terre qui n’est pas rassasiée d’eau et le feu qui ne dit jamais: Assez! (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
L’œil qui se moque d’un père, et qui dédaigne l’obéissance envers une mère, les corbeaux du torrent le perceront, et les petits de l’aigle le dévoreront.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Il y a trois choses qui me dépassent, et même quatre que je ne comprends pas:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
la trace de l’aigle dans les cieux, la trace du serpent sur le rocher, la trace du navire au milieu de la mer, et la trace de l’homme chez la jeune fille.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Telle est la voie de la femme adultère: elle mange et, s’essuyant la bouche, elle dit: « Je n’ai pas fait de mal. »
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Sous trois choses la terre tremble, et sous quatre, qu’elle ne peut supporter:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
sous un esclave lorsqu’il vient à régner, et un insensé lorsqu’il est rassasié de pain,
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
sous une femme dédaignée lorsqu’elle se marie, et sous une servante lorsqu’elle hérite de sa maîtresse.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Il y a sur la terre quatre animaux bien petits, et qui sont cependant très sages:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
Les fourmis, peuple sans force, préparent en été leur nourriture;
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
les damans, peuple sans puissance, placent leur gîte dans les rochers;
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
les sauterelles n’ont pas de roi, et elles sortent toutes par bandes;
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
tu peux prendre le lézard avec la main, et il se trouve dans le palais des rois.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Il y en a trois qui ont une belle allure, et quatre qui ont une belle démarche:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
le lion, le plus brave des animaux, ne reculant devant aucun adversaire;
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
l’animal aux reins agiles, ou le bouc, et le roi, à qui personne ne résiste.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Si tu es assez fou pour te laisser emporter par l’orgueil, et si tu en as la pensée, mets la main sur ta bouche,
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
car la pression du lait produit du beurre, la pression du nez produit du sang, et la pression de la colère produit la querelle. PAROLES DU ROI LAMUEL.

< Karin Magana 30 >