< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
These are sayings/messages that God gave to Agur, the son of Jakeh. [Agur wrote them] for Ithiel and Ucal.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
It seems that I am very stupid; I do not deserve to be considered to be a human; I do not have the good sense that humans should have.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
I have not learned [how to become] wise and I do not know [much] about God.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
[But let me say this]: No one [RHQ] has ascended to heaven [to find out what God is like] and returned [to tell us]. No one [RHQ] has gathered/held the wind in his hand. No one [RHQ] has wrapped the water [in the ocean] in [a piece of] cloth, and no one [RHQ] has established the boundaries of the earth. [If you know who has done those things, tell me] [RHQ] his name, and the names of his children [SAR]! [But you do not know who has done those things, so you cannot speak with authority about what God is like].
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Everything that God has said is true; he is [like] a shield [MET] for all those who request him to protect them.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Do not add to (OR, change) what God has said; if you do that, he will rebuke you and show that you are lying.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
[God], I ask you to do two things for me; [please] do them before I die:
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Help me never to lie or deceive [people] and do not cause me to become poor or to become rich. [Just] give me the food that I need;
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
because if I become rich, I might say that I do not [RHQ] know you and that I do not need you; and if I become poor, I might dishonor you by stealing things.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Do not (slander/say bad things about) a worker to his boss; if you do that, the worker will curse you, and cause you to have trouble.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
[I will list four kinds of evil things that people do]: Some people curse their fathers and do not [ask God to] bless their mothers.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
Some people think that they are perfect, but [really] they have never been cleansed from their guilt for committing disgusting sins.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
Some people are very proud; they think that they are very good and they despise others.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
Some people [act very cruelly toward others]; [it is as though] [MET] they have teeth that are [like] sharp knives; they severely oppress poor [people] and try to cause them to disappear from the land.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Leeches [are always wanting more blood to suck]; [similarly, greedy people are always] saying “Give [me some]!” or “Give [me more]!” [MET] There are four things that are never (satisfied/content with what they have); they always want more [LIT]:
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
The place where the dead people are; women who do not have any children; ground that needs water/rain; and a fire that always needs more wood. (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Those who [SYN] make fun of their fathers or refuse to obey their mothers (OR, despise their aged mothers) should [die and] have their eyes pecked out by crows, and the [rest of their corpses should be] fed to the vultures.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
There are four things that are wonderful to me, [but] I do not understand any of them:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
How eagles fly in the sky, how snakes [are able to] move/crawl across a big rock, how ships sail on the seas, and how a man falls in love with a woman.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
This is what a woman who (is not faithful to/does not have sex only with) her husband does: She commits adultery [EUP], and [then] bathes and says, “I have not done anything that is wrong!”
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
There are four things that no [one in] the world can tolerate:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
[What] a slave [does who] becomes a king, a foolish person eating [too much] food,
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
[what] a woman who is hated [does when she] gets married, and [what] a female servant [does when she] becomes the boss instead of her mistress.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
[There are] four animals on the earth that are small, but they are very wise:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
Ants are not strong, but they store up food during the summer [in order to have it during the winter].
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
Rock badgers [also] are not strong, but they make their homes among the rocks [where they will be safe].
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
Locusts do not have a king, but they march like [the soldiers in] an army.
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
Lizards/Geckos [are very small and] you can hold them in your hand, but they are [cleverly able to get] inside kings’ palaces.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
[There are] four animals that strut around and look very impressive while they walk [DOU]:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
Lions, which are stronger than all other animals and are not afraid of any of them;
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
male goats, strutting roosters, and kings who (parade/walk proudly back and forth) in front of the people whom they rule.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
If you have acted foolishly, exalting yourself, or if you been planning [to do something] evil, stop it immediately [IDM]!
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
If you churn milk, it produces butter/curds, and if you hit [someone hard on his] nose, [his nose] bleeds; similarly, if you do something to cause [people to become] angry, strife [usually] results.

< Karin Magana 30 >