< Karin Magana 30 >
1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Slova Agura, syna Jáke. Sepsání řečí muže toho k Itielovi, k Itielovi a Uchalovi.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Jistě žeť jsem hloupější nad jiné, tak že rozumnosti člověka obecného nemám,
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
Aniž jsem se naučil moudrosti, a umění svatých neumím.
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Kdo vstoupil v nebe, i sstoupil? Kdo sebral vítr do hrstí svých? Kdo shrnul vody v roucho své? Kdo upevnil všecky končiny země? Které jméno jeho, a jaké jméno syna jeho, víš-li?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Všeliká výmluvnost Boží přečištěná jest; onť jest štít doufajících v něho.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Nepřidávej k slovům jeho, aby tě nekáral, a byl bys ve lži postižen.
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Dvou věcí žádám od tebe, neoslýchejž mne, prvé než umru:
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Marnost a slovo lživé vzdal ode mne, chudoby neb bohatství nedávej mi, živ mne pokrmem vedlé potřeby mé,
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
Abych snad nasycen jsa, tě nezapřel, a neřekl: Kdo jest Hospodin? a abych zchudna, nekradl, a nebral naprázdno jména Hospodina Boha svého.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Nesoč na služebníka před pánem jeho, aťby nezlořečil, a ty abys nehřešil.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
Jest pokolení, kteréž otci svému zlořečí, a matce své nedobrořečí.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
Jest pokolení čisté samo u sebe, ačkoli od nečistot svých není obmyto.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
Jest pokolení, jehož vysoké jsou oči, a víčka jeho jsou vyzdvižená.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
Jest pokolení, jehož zubové jsou mečové, a třenovní zubové jeho nožové, k zžírání chudých na zemi a nuzných na světě.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Pijavice má dvě dcery říkající: Dej, dej. Tři věci nebývají nasyceny, anobrž čtyry, kteréž nikdy neřeknou: Dosti:
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol )
Peklo a život neplodné, země též nebývá nasycena vodou, a oheň neříká: Dosti. (Sheol )
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Oko, kteréž se posmívá otci, a pohrdá poslušenstvím matky, vyklubí krkavci potoční, aneb snědí je orličata.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Tři tyto věci skryty jsou přede mnou, nýbrž čtyry, kterýchž neznám:
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
Cesty orlice v povětří, cesty hada na skále, cesty lodí u prostřed moře, a cesty muže při panně.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Takováž jest cesta ženy cizoložné: Jí, a utře ústa svá, a dí: Nepáchala jsem nepravosti.
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Pode třmi věcmi pohybuje se země, anobrž pod čtyřmi, jichž nemůž snésti:
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
Pod služebníkem, když kraluje, a bláznem, když se nasytí chleba;
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
Pod omrzalou, když se vdá, a děvkou, když dědičkou bývá paní své.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Čtyry tyto věci jsou malé na zemi, a však jsou moudřejší nad mudrce:
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
Mravenci, lid nesilný, kteříž však připravují v létě pokrm svůj;
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
Králíkové, lid nesilný, kteříž však stavějí v skále dům svůj;
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
Krále nemají kobylky, a však vycházejí po houfích všecky;
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
Pavouk rukama dělá, a bývá na palácích královských.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Tři tyto věci udatně vykračují, anobrž čtyry, kteréž zmužile chodí:
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
Lev nejsilnější mezi zvířaty, kterýž neustupuje před žádným;
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
Přepásaný na bedrách kůň neb kozel, a král, proti němuž žádný nepovstává.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Jestliže jsi bláznil, vynášeje se, a myslil-lis zle, ruku na ústa polož.
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
Kdo tluče smetanu, stlouká máslo, a stiskání nosu vyvodí krev, tak popouzení k hněvu vyvodí svár.