< Karin Magana 30 >

1 Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
Goe da gogolole sia: su A: ige (Ya: ige egefe) da amane sia: i, “Gode da namagai hame! Gode da namagai hame! Na da gasa hame hahani galebe.
2 “Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
Na da dunu agoai hame. Na da ohe agoai esala. Dunu da dawa: su noga: iwane dialumu da defea. Be na da agoaiwane dawa: su da hame galebe.
3 Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
Na da bagade dawa: su hamedafa lai amola na da Gode ea hou hamedafa dawa:
4 Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
Nowa da Hebene hou huluane dawa: bela: ? Nowa da fo ea loboga gagubala: ? Amola nowa da abula gadelaiga hano gadoba: bela: ? Amola osobo bagade ea bega: huluane da nowa ea alalo ilegebela: ? Amola dia dawa: loba, e da nowala: ? Amola e da nowa ea manola: ?
5 “Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
Gode E da Ea moloidafa hou hamomu ilegele sia: i, E da dafawane hamomu. Amola, E da Gaga: sudafa, amola nowa dunu da E hogoi helesea, amo dunu da gaga: su ba: mu.
6 Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Gode Ea sia: dafa amoga dia hanai sia: mae gilisima. Di da amane hamosea, E da dima gagabomu, amola eno dunu dawa: ma: ne Gode da di da ogogole olelesu dunu olelemu.”
7 “Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
Na da Dima adole ba: sa, “Gode! Na da liligi aduna Dima lalalu bogomu da defea.
8 Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
Na ogogolalosa: besa: le, na Dia fidima. Na bagade gagui agoai esalosa: besa: le o hamedafa gagui agoai esalosa: besa: le, Dia na fidima. Amaiba: le, ha: i manu na dafawane esaloma: ne lamu liligi defele nama ima.
9 In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
Na da Di gogolesa: besa: le, liligi bagadedafa nama mae ima. Amola na da liligi hamedafa gaguiba: le, wamolasa: besa: le amola Dia Dio wadela: sa: besa: le, liligi fonobahadi nama ima.
10 “Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
Di da hawa: hamosu dunu amo ea hou ea hina dunuma baligidu sia: mae sia: ma. Amane hamosea, hawa: hamosu dunu da dima gagabumu, amola dia hamoi defele, di da se nabimu.
11 “Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
Dunu oda ilia da eda se nabima: ne, gagabusa. Amola eme amoma nodone hame asigisa.
12 waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
Dunu oda ilia da amane dawa: sa, ilisu ilia da moloiwaneyale dawa: sa. Be ilia da ledodafa gala.
13 waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
Goe da dunu eno ilia da amane dawa: su, ilia da ili da moloiwaneyale dawa: su. Dafawane! Ilia da ilisu noga: iwaneyale dawa: sa.
14 waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
Amola dunu oda da hame gagui dunu ilima bagadewane ogogosa amola wadela: lesimusa: dawa: sa. Ilia da amodili ilia esalusu ba: sa.
15 “Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
Hebe da idiwi aduna gala. Ela da dio afadafa gala, amo ‘Nama ima!’ Amola liligi biyaduyale amo ilia hanai da hame sadimu.
16 Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
Amo liligi biyaduyale gala da, (age) Bogoi uli dogoi da hame sadimu. (ageyadu) Aligime uda da hame sadimu. (osoda) Hafoga: i osobo gibu hameba: le da hame sadimu. (biyadu) Amola lalu haba: domu gogolei amo da hame sadimu. (Sheol h7585)
17 “Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
Nowa da eda amoma lasogole ofesega: sea, o ea eme ea da: i hamoi eso amoga ema higale ba: sea, sia misini ea da: i hodo manu da defea, amola soge buhiba amo ea si duga: mu da defea.
18 “Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
Eno liligi biyaduyale gala amo na dawa: mu gogolei.
19 yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
Goe da wayalima muagadodafa hagili ahoa. Sania da gele da: iya sugi ahoana. Eno da dusagai hano wayabo amo ganodini masusa: logo hogolala. Dunu amola uda ela lamusa: magedaha.
20 “Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
Goe da uda amo da egoama baligi fa: su, amo ea hou da agoaiwane gala. E da inia dunu adole lale, ha: i nanu, ea lafi dagale, amane sia: sa, “Na da wadela: le hame hamoi.”
21 “Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
Liligi biyaduyale gala da wadela: idafaba: le, fedege agoane, osobo bagade da amo liligi biyaduyale gala higasa.
22 bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
(age) Udigili hawa: hamosu dunu e da hina bagade hamosa. (ageyadu) Gagaousu dunu da ha: i manu bagade nawene sadisa.
23 macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
(osoda) Wadela: idafa uda amo da gawa fisa. (biyadu) Hawa: hamosu uda da ea hina uda amo ea sogebi samogene lasa.
24 “Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
Osobo bagadega da ohe fonobahadidafa biyaduyale gala. Amo ohe amo da baligili bagadedafa dawa: su gala.
25 Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
(age) Gedama! Amo da liligi fonobahadi amola gasa hame. Be amomane ilia da mugi oubiga ha: i manu momagesa.
26 remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
(ageyadu) Amola wasigiba ea hou dawa: ma. E da gasa hame be amomane e da diasu igi adoba gagusa.
27 fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
(osoda) Amola danuba: dawa: ma. Ilia da hina hame, amomane ilia da gilisili hagili mogodigili ahoa.
28 ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
(biyadu) Amola goma: fi ilia hou dawa: ma. Amo da liligi fonobahadi amola dia da lobo afaega gagumusa: dawa: Be ilia da hina bagade ea diasu noga: i amo ganodini esalebe ba: sa.
29 “Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
Liligi biyaduyale gala ilia ahoabe hou di ba: sea, noga: iwane ba: sa.
30 zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
Amo liligi biyaduyale gala da (age) Laione wa: me e da gasa bagade amola ohe enoga e baligimu da hamedei. Amola e da ohe enoba: le hame beda: sa.
31 zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
(ageyadu) Goudi (osoda) Gagala gawali amo ilia da dada: lole ahoa, amola (biyadu) Hina bagade dunu ilia da ilia dunu fi ilia midadi ahoa.
32 “In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
Amola di da gagousu dunu agoai, gasa fi hou hamosea, amola wadela: i hou hamomusa: dawa: sea, yolesima amola dawa: ma.
33 Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”
Amola dia ohe amo ea dodo maga: me biogosea, amo da bu sefe hamomu. Amola dia eno ea mia fasea, heale masunu. Amola dia da nenege degesea, se nabasu da dima doaga: mu.

< Karin Magana 30 >