< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mwanangu, usizisahau amri zangu na uyatunze mafundisho yangu katika moyo wako,
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
maana ziatakuongezea siku zako na miaka ya maisha yako na amani.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Usiache utiifu wa agano na uaminifu viondoke kwako, vifunge katika shingo yako, viandike katika vibao vya moyo wako.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Ndipo utapata kibali na heshima mbele Mungu na wanadamu.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Mtegemee Yehova kwa moyo wako wote na wala usitegemee ufahamu wako mwenyewe,
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
katika njia zako zote mkiri Yeye na yeye atayanyosha mapito yako.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Usiwe mwenye busara machoni pako mwenyewe; mche Yehova na jiepushe na uovu.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Itakuponya mwili wako na kukuburudisha mwili wako.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Mheshimu Yehova kwa utajiri wako na kwa malimbuko ya mazao kwa kila unachozalisha,
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
na ndipo ghala zako zitajaa na mapipa makubwa yatafurika kwa divai mpya.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mwanangu, usidharau kuadibishwa na Yohova na wala usichukie karipio lake,
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
maana Yehova huwaadibisha wale wapendao, kama baba anavyoshughulika kwa mtoto wake ampendezaye.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Yeye apataye hekima anafuraha, naye hupata ufahamu.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Kwani katika hekima unapata manufaa kuliko ukibadilisha kwa fedha na faida yake inafaa zaidi kuliko dhahabu.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Hekima inathamani zaidi kuliko kito, na hakuna unachokitamani kinaweza kulinganishwa na hekima.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Yeye anasiku nyingi katika mkono wake wa kuume; na mkono wake wa kushoto ni utajiri na heshima.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Njia zake ni njia za ukarimu na mapito yake ni amani.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Yeye ni mti wa uzima kwa wale wanaomshikilia, wale wanaomshikilia wanafuraha.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Kwa hekima Yehova aliweka msingi wa dunia, kwa ufahamu aliziimarisha mbingu.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Kwa maarifa yake vina vilipasuka na mawingu kudondosha umande wake.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mwanangu, zingatia hukumu ya kweli na ufahamu, na wala usiache kuvitazama.
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Vitakuwa uzima wa nafsi yako na urembo wa hisani wa kuvaa shingoni mwako.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Ndipo utatembea katika njia yako kwa usalama na mguu wako hautajikwaa;
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
ulalapo hutaogopa; utakapolala, usingizi wako utakuwa mtamu.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Usitishwe na hofu ya ghafula au uharibifu uliosababishwa na waovu unapotokea,
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
kwa maana Yehova utakuwa upande wako na ataulinda mguu wako usinaswe kwenye mtego.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Usizuie mema kwa wale wanaoyastahili, wakati utendaji upo ndani ya mamlaka yako.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Jirani yako usimwambie, “Nenda, na uje tena, na kesho nitakupa,” wakati pesa unazo.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Usiweke mpango wa kumdhuru jirani yako- anayeishi jirani nawe na yeye anakuamini.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Usishindane na mtu pasipo sababu, ikiwa hajafanya chochote kukudhuru.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Usimhusudu mtu jeuri au kuchagua njia zake zozote.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Maana mtu mjanja ni chukizo kwa Yehova, bali humleta mtu mwaminifu kwenye tumaini lake.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Laana ya Yehova ipo katika nyumba ya watu waovu, bali huibariki maskani ya watu wenye haki.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Yeye huwadhihaki wenye dhihaka, bali huwapa hisani watu wanyenyekevu.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Watu wenye busara huirithi heshima, bali wapumbavu huinuliwa kwa fedheha yao wenyewe.

< Karin Magana 3 >