< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mwanangu, usisahau mafundisho yangu, bali zitunze amri zangu moyoni mwako,
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
kwa kuwa zitakuongezea miaka mingi ya maisha yako na kukuletea mafanikio.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Usiache kamwe upendo na uaminifu vitengane nawe; vifunge shingoni mwako, viandike katika ubao wa moyo wako.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Ndipo utapata kibali na jina zuri mbele za Mungu na mwanadamu.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Mtumaini Bwana kwa moyo wako wote wala usizitegemee akili zako mwenyewe;
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
katika njia zako zote mkiri yeye, naye atayanyoosha mapito yako.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Usiwe mwenye hekima machoni pako mwenyewe; mche Bwana ukajiepushe na uovu.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Hii itakuletea afya mwilini mwako, na mafuta kwenye mifupa yako.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Mheshimu Bwana kwa mali zako na kwa malimbuko ya mazao yako yote;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
ndipo ghala zako zitakapojaa hadi kufurika, viriba vyako vitafurika kwa mvinyo mpya.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mwanangu, usiidharau adhabu ya Bwana na usichukie kukaripiwa naye,
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
kwa sababu Bwana huwaadibisha wale awapendao, kama vile baba afanyavyo kwa mwana apendezwaye naye.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Heri mtu yule aonaye hekima, mtu yule apataye ufahamu,
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
kwa maana hekima ana faida kuliko fedha na mapato yake ni bora kuliko ya dhahabu safi.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Hekima ana thamani kuliko marijani; hakuna chochote unachokitamani kinachoweza kulinganishwa naye.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Maisha marefu yako katika mkono wake wa kuume; katika mkono wake wa kushoto kuna utajiri na heshima.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Njia zake zinapendeza, mapito yake yote ni amani.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Yeye ni mti wa uzima kwa wale wanaomkumbatia; wale wamshikao watabarikiwa.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Kwa hekima Bwana aliiweka misingi ya dunia, kwa ufahamu aliziweka mbingu mahali pake;
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
kwa maarifa yake vilindi viligawanywa, nayo mawingu yanadondosha umande.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mwanangu, hifadhi maamuzi mema na busara, usiache vitoke machoni pako;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
ndipo vitakapokuwa uzima nafsini mwako na pambo la neema shingoni mwako.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Kisha utaenda katika njia yako salama, wala mguu wako hautajikwaa;
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
ulalapo, hautaogopa; ulalapo usingizi wako utakuwa mtamu.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Usiogope maafa ya ghafula au maangamizi yanayowapata waovu,
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
kwa kuwa Bwana atakuwa tumaini lako na kuepusha mguu wako kunaswa katika mtego.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Usizuie wema kwa wale wanaostahili ikiwa katika uwezo wako kutenda.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Usimwambie jirani yako, “Njoo baadaye, nitakupa kesho”: wakati wewe unacho kitu kile karibu nawe.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Usifanye hila ya kumdhuru jirani yako, ambaye anaishi karibu na wewe akikuamini.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Usimshtaki mtu bila sababu, wakati hajakutenda dhara lolote.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Usimwonee wivu mtu mwenye jeuri wala kuchagua njia yake iwayo yote,
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
kwa kuwa Bwana humchukia mtu mpotovu, lakini siri yake iko kwa mwenye haki.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Laana ya Bwana i juu ya nyumba ya mwovu, lakini yeye huibariki nyumba ya mwenye haki.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Huwadhihaki wale wanaodhihaki, lakini huwapa neema wale wanyenyekevu.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Wenye hekima hurithi heshima, bali huwaaibisha wapumbavu.

< Karin Magana 3 >