< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Hijo mío, no olvides mis enseñanzas, Y tu corazón guarde mis mandamientos.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Porque largura de días, años de vida Y paz te aumentarán.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Nunca se aparten de ti la misericordia y la verdad. Átalas a tu cuello. Escríbelas en la tabla de tu corazón,
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Y hallarás gracia y buena opinión Ante los ojos de ʼElohim y del hombre.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Confía en Yavé con todo tu corazón, Y no te apoyes en tu propia inteligencia.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Reconócelo en todos tus caminos, Y Él enderezará tus sendas.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
No seas sabio en tu propia opinión. Teme a Yavé Y apártate del mal,
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Porque será medicina a tu ombligo Y tuétano a tus huesos.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honra a Yavé con tus bienes Y con las primicias de todos tus frutos.
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
Tus graneros se henchirán de abundancia, Y tus lagares rebosarán de mosto.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Hijo mío, no menosprecies el castigo de Yavé, Ni te fatigues de su corrección.
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Porque Yavé disciplina al que ama, Como el padre al hijo en quien se complace.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Inmensamente feliz el hombre que halla sabiduría Y el que obtiene la inteligencia.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Porque su provecho es mayor que el de la plata, Y su resultado es mejor que el oro fino.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Es más preciosa que las perlas, Nada de lo que desees podrá compararse con ella.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Abundancia de días hay en su mano derecha, Y en su izquierda, riquezas y honra.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Sus caminos son agradables, Y en todas sus sendas hay paz.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Es árbol de vida a los que echan mano a ella, Y los que la retienen son inmensamente felices.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Yavé fundó la tierra con sabiduría Y con entendimiento afirmó los cielos.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Con su conocimiento fueron divididos los océanos Y las nubes destilan rocío.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Hijo mío, no se aparten estas cosas de tus ojos. Guarda la sabiduría y la discreción,
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Y serán vida a tu alma y gracia a tu cuello.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Entonces andarás con seguridad en tu camino Y tu pie no tropezará.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Cuando te acuestas, no tendrás temor. Te acostarás, Y tu sueño será dulce.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
No temerás el pavor repentino, Ni cuando llega el ataque de los perversos,
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Porque Yavé será tu Confianza. Él guardará tu pie de caer en la trampa.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
No retengas el bien a quien es debido, Cuando tienes el poder para hacerlo.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
No digas a tu prójimo: Anda y vuelve, mañana te lo daré, Cuando tienes contigo qué darle.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
No trames el mal contra el prójimo Que habita confiado junto a ti.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
No tengas pleito con alguno sin causa, Si no te hizo agravio.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
No envidies al hombre violento, Ni escojas alguno de sus caminos,
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Porque Yavé aborrece al perverso. Su íntima comunión es con los rectos.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
La maldición de Yavé está sobre la casa del impío, Pero bendice la morada de los justos.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Ciertamente Él se burla de los que se burlan Y da gracia a los humildes.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Los sabios heredarán honra, Pero los necios cargarán la afrenta.