< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Filho meu, não te esqueças da minha lei, e o teu coração guarde os meus mandamentos.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Porque eles te acrescentarão longura de dias, e anos de vida e paz.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Não te desamparem a benignidade e a fidelidade: ata-as ao teu pescoço; escreve-as na táboa do teu coração.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
E acharás graça e bom entendimento aos olhos de Deus e dos homens.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Confia no Senhor com todo o teu coração, e não te estribes no teu próprio entendimento.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Reconhece-o em todos os teus caminhos, e ele endireitará as tuas veredas.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Não sejas sábio a teus próprios olhos: teme ao Senhor e aparta-te do mal.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Isto será saúde para o teu umbigo, e regadura para os teus ossos.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honra ao Senhor com a tua fazenda, e com as primícias de toda a tua renda.
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
E se encherão os teus celeiros de fartura, e trasbordarão de mosto os teus lagares.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Filho meu, não rejeites a correção do Senhor, nem te enojes da sua repreensão.
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Porque o Senhor repreende aquele a quem ama, assim como o pai ao filho a quem quer bem.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Bem-aventurado o homem que acha sabedoria, e o homem que produz inteligência.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Porque melhor é a sua mercadoria do que a mercadoria de prata, e a sua renda do que o ouro mais fino.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Mais preciosa é do que os rubins, e tudo o que mais podes desejar não se pode comparar a ela.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Longura de dias há na sua mão direita: na sua esquerda riquezas e honra.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Os caminhos dela são caminhos de delícias, e todas as suas veredas paz.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
É árvore da vida para os que dela pegam, e bem-aventurados são todos os que a reteem.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
O Senhor com sabedoria fundou a terra: preparou os céus com entendimento.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Pelo seu conhecimento se fenderam os abismos, e as nuvens destilam o orvalho.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Filho meu, não se apartem estes dos teus olhos: guarda a verdadeira sabedoria e o bom siso;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Porque serão vida para a tua alma, e graça para o teu pescoço.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Então andarás com confiança pelo teu caminho, e não tropeçará o teu pé.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Quando te deitares, não temerás: mas te deitarás e o teu sono será suave.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Não temas o pavor repentino, nem a assolação dos ímpios quando vier.
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Porque o Senhor será a tua esperança, e guardará os teus pés de os prenderem.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Não detenhas dos seus donos o bem, tendo na tua mão poder faze-lo.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Não digas ao teu próximo: vai, e torna, e amanhã to darei: tendo-o tu contigo.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Não maquines mal contra o teu próximo, pois habita contigo confiadamente.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Não contendas contra alguém sem razão, se te não tem feito mal.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Não tenhas inveja do homem violento, nem elejas algum de seus caminhos.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Porque o perverso é abominação ao Senhor, mas com os sinceros está o seu segredo.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
A maldição do Senhor habita na casa do ímpio, mas à habitação dos justos abençoará.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Certamente ele escarnecerá dos escarnecedores, mas dará graça aos mansos.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Os sábios herdarão honra, porém os loucos tomam sobre si confusão.