< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
ای پسر من، تعلیم مرا فراموش مکن و دل تو اوامر مرا نگاه دارد،۱
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
زیرا که طول ایام وسالهای حیات و سلامتی را برای تو خواهدافزود.۲
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
زنهار که رحمت و راستی تو را ترک نکند. آنها را بر گردن خود ببند و بر لوح دل خودمرقوم دار.۳
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
آنگاه نعمت و رضامندی نیکو، درنظر خدا و انسان خواهی یافت.۴
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
به تمامی دل خود بر خداوند توکل نما و بر عقل خود تکیه مکن.۵
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
در همه راههای خود او را بشناس، و اوطریقهایت را راست خواهد گردانید.۶
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
خویشتن را حکیم مپندار، از خداوند بترس و از بدی اجتناب نما.۷
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
این برای ناف تو شفا، وبرای استخوانهایت مغز خواهد بود.۸
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
از مایملک خود خداوند را تکریم نما و از نوبرهای همه محصول خویش.۹
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
آنگاه انبارهای تو به وفورنعمت پر خواهد شد، و چرخشتهای تو از شیره انگور لبریز خواهد گشت.۱۰
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
‌ای پسر من، تادیب خداوند را خوار مشمار، و توبیخ او را مکروه مدار.۱۱
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
زیرا خداوند هر‌که را دوست داردتادیب می‌نماید، مثل پدر پسر خویش را که از اومسرور می‌باشد.۱۲
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
خوشابحال کسی‌که حکمت را پیدا کند، و شخصی که فطانت را تحصیل نماید.۱۳
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
زیرا که تجارت آن از تجارت نقره ومحصولش از طلای خالص نیکوتر است.۱۴
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
ازلعلها گرانبهاتر است و جمیع نفایس تو با آن برابری نتواند کرد.۱۵
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
به‌دست راست وی طول ایام است، و به‌دست چپش دولت و جلال.۱۶
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
طریقهای وی طریقهای شادمانی است و همه راههای وی سلامتی می‌باشد.۱۷
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
به جهت آنانی که او را به‌دست گیرند، درخت حیات‌است وکسی‌که به او متمسک می‌باشد خجسته است.۱۸
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
خداوند به حکمت خود زمین را بنیاد نهاد، و به عقل خویش آسمان را استوار نمود.۱۹
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
به علم او لجه‌ها منشق گردید، و افلاک شبنم رامی چکانید.۲۰
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
‌ای پسر من، این چیزها از نظر تودور نشود. حکمت کامل و تمیز را نگاه دار.۲۱
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
پس برای جان تو حیات، و برای گردنت زینت خواهد بود.۲۲
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
آنگاه در راه خود به امنیت سالک خواهی شد، و پایت نخواهد لغزید.۲۳
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
هنگامی که بخوابی، نخواهی ترسید و چون دراز شوی خوابت شیرین خواهد شد.۲۴
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
از خوف ناگهان نخواهی ترسید، و نه از خرابی شریران چون واقع شود.۲۵
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
زیرا خداوند اعتماد تو خواهد بود و پای تو را از دام حفظ خواهد نمود.۲۶
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
احسان را ازاهلش باز مدار، هنگامی که بجا آوردنش در قوت دست توست.۲۷
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
به همسایه خود مگو برو وبازگرد، و فردا به تو خواهم داد، با آنکه نزد توحاضر است.۲۸
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
بر همسایه ات قصد بدی مکن، هنگامی که او نزد تو در امنیت ساکن است.۲۹
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
باکسی‌که به تو بدی نکرده است، بی‌سبب مخاصمه منما.۳۰
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
بر مرد ظالم حسد مبر وهیچکدام از راههایش را اختیار مکن.۳۱
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
زیراکج خلقان نزد خداوند مکروهند، لیکن سر او نزدراستان است،۳۲
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
لعنت خداوند بر خانه شریران است. اما مسکن عادلان را برکت می‌دهد.۳۳
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
یقین که مستهزئین را استهزا می‌نماید، اما متواضعان رافیض می‌بخشد.۳۴
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
حکیمان وارث جلال خواهند شد، اما احمقان خجالت را خواهند برد.۳۵

< Karin Magana 3 >