< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Min sønn! Glem ikke min lære og la ditt hjerte bevare mine bud!
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
For langt liv og mange leveår og fred skal de gi dig i rikt mål.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
La ikke kjærlighet og trofasthet vike fra dig, bind dem om din hals, skriv dem på ditt hjertes tavle!
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Så skal du finne nåde og få god forstand i Guds og menneskers øine.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Sett din lit til Herren av hele ditt hjerte, og stol ikke på din forstand!
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Tenk på ham på alle dine veier! Så skal han gjøre dine stier rette.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Vær ikke vis i egne øine, frykt Herren og vik fra det onde!
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Det skal være lægedom for din kropp og gi ny styrke til dine ben.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Ær Herren med gaver av ditt gods og med førstegrøden av all din avling!
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
Så skal dine lader fylles med overflod og dine persekar flyte over av most.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Min sønn! Forakt ikke Herrens tukt og vær ikke utålmodig når han refser dig!
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
For den Herren elsker, ham refser han, som en far refser den sønn han har kjær.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Salig er det menneske som har funnet visdom, det menneske som vinner forstand;
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
for det er bedre å vinne den enn å vinne sølv, og det utbytte den gir, er bedre enn gull.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Den er kosteligere enn perler, og alle dine skatter kan ikke lignes med den.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Langt liv har den i sin høire hånd, rikdom og ære i sin venstre.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Dens veier er fagre veier, og alle dens stier fører til lykke.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Den er et livsens tre for dem som griper den, og hver den som holder fast på den, må prises lykkelig.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Herren grunnfestet jorden med visdom; han bygget himmelen med forstand.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Ved hans kunnskap vellet de dype vann frem, og ved den lar skyene dugg dryppe ned.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Min sønn! La dem ikke vike fra dine øine, bevar visdom og klokskap!
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Så skal de være liv for din sjel og pryd for din hals.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Da skal du vandre din vei trygt og ikke støte din fot.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Når du legger dig, skal du ikke frykte, og når du har lagt dig, skal din søvn være søt.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Da trenger du ikke å være redd for uventet skrekk, eller for uværet når det kommer over de ugudelige!
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
For Herren skal være din tillit, og han skal bevare din fot fra å fanges.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Nekt ikke de trengende din hjelp, når det står i din makt å gi den!
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Si ikke til din næste: Gå bort og kom igjen, jeg skal gi dig imorgen - når du kan gjøre det straks!
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Legg ikke op onde råd mot din næste, når han kjenner sig trygg hos dig!
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Trett ikke med et menneske uten årsak, når han ikke har gjort dig noget ondt!
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Misunn ikke en voldsmann, og velg ikke nogen av alle hans veier!
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
For en falsk mann er en vederstyggelighet for Herren, men med de opriktige har han fortrolig samfund.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Herrens forbannelse er over den ugudeliges hus, men de rettferdiges bolig velsigner han.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Spotterne spotter han, men de ydmyke gir han nåde.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
De vise arver ære, men dårene får skam til lønn.

< Karin Magana 3 >