< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Fili mi, ne obliviscaris legis meæ, et præcepta mea cor tuum custodiat.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Longitudinem enim dierum, et annos vitæ, et pacem apponent tibi.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Misericordia, et veritas te non deserant, circumda eas gutturi tuo, et describe in tabulis cordis tui:
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
et invenies gratiam, et disciplinam bonam coram Deo et hominibus.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Habe fiduciam in Domino ex toto corde tuo, et ne innitaris prudentiæ tuæ.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
In omnibus viis tuis cogita illum, et ipse diriget gressus tuos.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Ne sis sapiens apud temetipsum: time Deum, et recede a malo:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
sanitas quippe erit umbilico tuo, et irrigatio ossium tuorum.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honora Dominum de tua substantia, et de primitiis omnium frugum tuarum da ei:
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
et implebuntur horrea tua saturitate, et vino torcularia tua redundabunt.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Disciplinam Domini, fili mi, ne abiicias: nec deficias cum ab eo corriperis:
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
quem enim diligit Dominus, corripit: et quasi pater in filio complacet sibi.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Beatus homo, qui invenit sapientiam, et qui affluit prudentia:
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
melior est acquisitio eius negotiatione argenti, et auri primi et purissimi fructus eius:
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
pretiosior est cunctis opibus: et omnia, quæ desiderantur, huic non valent comparari.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Longitudo dierum in dextera eius, et in sinistra illius divitiæ, et gloria.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Viæ eius viæ pulchræ, et omnes semitæ illius pacificæ.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Lignum vitæ est his, qui apprehenderint eam: et qui tenuerit eam, beatus.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Dominus sapientia fundavit terram, stabilivit cælos prudentia.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Sapientia illius eruperunt abyssi, et nubes rore concrescunt.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Fili mi, ne effluant hæc ab oculis tuis: Custodi legem atque consilium:
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
et erit vita animæ tuæ, et gratia faucibus tuis.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Tunc ambulabis fiducialiter in via tua, et pes tuus non impinget:
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
si dormieris, non timebis: quiesces, et suavis erit somnus tuus.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Ne paveas repentino terrore, et irruentes tibi potentias impiorum.
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Dominus enim erit in latere tuo, et custodiet pedem tuum ne capiaris.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Noli prohibere benefacere eum, qui potest: si vales, et ipse benefac:
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Ne dicas amico tuo: Vade, et revertere: cras dabo tibi: cum statim possis dare.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Ne moliaris amico tuo malum, cum ille in te habeat fiduciam.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Ne contendas adversus hominem frustra, cum ipse tibi nihil mali fecerit.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Ne æmuleris hominem iniustum, nec imiteris vias eius:
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
quia abominatio Domini est omnis illusor, et cum simplicibus sermocinatio eius.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Egestas a Domino in domo impii: habitacula autem iustorum benedicentur.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Ipse deludet illusores, et mansuetis dabit gratiam.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Gloriam sapientes possidebunt: stultorum exaltatio, ignominia.

< Karin Magana 3 >