< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mein Sohn, vergiß nicht meine Belehrung, und dein Herz bewahre meine Gebote.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Denn Länge der Tage und Jahre des Lebens und Frieden werden sie dir mehren. -
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Güte und Wahrheit mögen dich nicht verlassen; binde sie um deinen Hals, schreibe sie auf die Tafel deines Herzens;
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
so wirst du Gunst finden und gute Einsicht in den Augen Gottes und der Menschen. -
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Vertraue auf Jehova mit deinem ganzen Herzen, und stütze dich nicht auf deinen Verstand.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Erkenne ihn auf allen deinen Wegen, und er wird gerade machen deine Pfade. -
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Sei nicht weise in deinen Augen, fürchte Jehova und weiche vom Bösen:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
es wird Heilung sein für deinen Nabel und Saft für deine Gebeine. -
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Ehre Jehova von deinem Vermögen und von den Erstlingen all deines Ertrages;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
so werden deine Speicher sich füllen mit Überfluß, und deine Kufen von Most überfließen.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mein Sohn, verwirf nicht die Unterweisung Jehovas, und laß dich seine Zucht nicht verdrießen.
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Denn wen Jehova liebt, den züchtigt er, und zwar wie ein Vater den Sohn, an dem er Wohlgefallen hat. -
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Glückselig der Mensch, der Weisheit gefunden hat, und der Mensch, der Verständnis erlangt!
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Denn ihr Erwerb ist besser als der Erwerb von Silber, und ihr Gewinn besser als feines Gold;
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
kostbarer ist sie als Korallen, und alles, was du begehren magst, kommt ihr an Wert nicht gleich.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Länge des Lebens ist in ihrer Rechten, in ihrer Linken Reichtum und Ehre.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Ihre Wege sind liebliche Wege, und alle ihre Pfade sind Frieden.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Ein Baum des Lebens ist sie denen, die sie ergreifen, und wer sie festhält, ist glückselig.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Jehova hat durch Weisheit die Erde gegründet, und durch Einsicht die Himmel festgestellt.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Durch seine Erkenntnis sind hervorgebrochen die Tiefen, und die Wolken träufelten Tau herab. -
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mein Sohn, laß sie nicht von deinen Augen weichen, bewahre klugen Rat und Besonnenheit;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
so werden sie Leben sein für deine Seele und Anmut deinem Halse.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Dann wirst du in Sicherheit deinen Weg gehen, und dein Fuß wird nicht anstoßen.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Wenn du dich niederlegst, wirst du nicht erschrecken; und liegst du, so wird dein Schlaf süß sein.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Fürchte dich nicht vor plötzlichem Schrecken, noch vor der Verwüstung der Gesetzlosen, wenn sie kommt;
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
denn Jehova wird deine Zuversicht sein, und wird deinen Fuß vor dem Fange bewahren.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Enthalte kein Gutes dem vor, welchem es zukommt, wenn es in der Macht deiner Hand steht, es zu tun. -
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Sage nicht zu deinem Nächsten: Geh hin und komm wieder, und morgen will ich geben! da es doch bei dir ist. -
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Schmiede nichts Böses wider deinen Nächsten, während er vertrauensvoll bei dir wohnt. -
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Hadere nicht mit einem Menschen ohne Ursache, wenn er dir nichts Böses angetan hat. -
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Beneide nicht den Mann der Gewalttat, und erwähle keinen von seinen Wegen. -
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Denn der Verkehrte ist Jehova ein Greuel, aber sein Geheimnis ist bei den Aufrichtigen.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Der Fluch Jehovas ist im Hause des Gesetzlosen, aber er segnet die Wohnung der Gerechten.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Fürwahr, der Spötter spottet er, den Demütigen aber gibt er Gnade.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Die Weisen erben Ehre, aber die Toren erhöht die Schande.

< Karin Magana 3 >