< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mon fils, n’oublie pas mes enseignements, Et que ton cœur garde mes préceptes;
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Car ils prolongeront les jours et les années de ta vie, Et ils augmenteront ta paix.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Que la bonté et la fidélité ne t’abandonnent pas; Lie-les à ton cou, écris-les sur la table de ton cœur.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Tu acquerras ainsi de la grâce et une raison saine, Aux yeux de Dieu et des hommes.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Confie-toi en l’Éternel de tout ton cœur, Et ne t’appuie pas sur ta sagesse;
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Reconnais-le dans toutes tes voies, Et il aplanira tes sentiers.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Ne sois point sage à tes propres yeux, Crains l’Éternel, et détourne-toi du mal:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Ce sera la santé pour tes muscles, Et un rafraîchissement pour tes os.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honore l’Éternel avec tes biens, Et avec les prémices de tout ton revenu:
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
Alors tes greniers seront remplis d’abondance, Et tes cuves regorgeront de moût.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mon fils, ne méprise pas la correction de l’Éternel, Et ne t’effraie point de ses châtiments;
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Car l’Éternel châtie celui qu’il aime, Comme un père l’enfant qu’il chérit.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Heureux l’homme qui a trouvé la sagesse, Et l’homme qui possède l’intelligence!
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Car le gain qu’elle procure est préférable à celui de l’argent, Et le profit qu’on en tire vaut mieux que l’or;
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Elle est plus précieuse que les perles, Elle a plus de valeur que tous les objets de prix.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Dans sa droite est une longue vie; Dans sa gauche, la richesse et la gloire.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Ses voies sont des voies agréables, Et tous ses sentiers sont paisibles.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Elle est un arbre de vie pour ceux qui la saisissent, Et ceux qui la possèdent sont heureux.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
C’est par la sagesse que l’Éternel a fondé la terre, C’est par l’intelligence qu’il a affermi les cieux;
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
C’est par sa science que les abîmes se sont ouverts, Et que les nuages distillent la rosée.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mon fils, que ces enseignements ne s’éloignent pas de tes yeux, Garde la sagesse et la réflexion:
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Elles seront la vie de ton âme, Et l’ornement de ton cou.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Alors tu marcheras avec assurance dans ton chemin, Et ton pied ne heurtera pas.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Si tu te couches, tu seras sans crainte; Et quand tu seras couché, ton sommeil sera doux.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Ne redoute ni une terreur soudaine, Ni une attaque de la part des méchants;
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Car l’Éternel sera ton assurance, Et il préservera ton pied de toute embûche.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Ne refuse pas un bienfait à celui qui y a droit, Quand tu as le pouvoir de l’accorder.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Ne dis pas à ton prochain: Va et reviens, Demain je donnerai! Quand tu as de quoi donner.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Ne médite pas le mal contre ton prochain, Lorsqu’il demeure tranquillement près de toi.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Ne conteste pas sans motif avec quelqu’un, Lorsqu’il ne t’a point fait de mal.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Ne porte pas envie à l’homme violent, Et ne choisis aucune de ses voies.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Car l’Éternel a en horreur les hommes pervers, Mais il est un ami pour les hommes droits;
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
La malédiction de l’Éternel est dans la maison du méchant, Mais il bénit la demeure des justes;
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Il se moque des moqueurs, Mais il fait grâce aux humbles;
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Les sages hériteront la gloire, Mais les insensés ont la honte en partage.