< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mon fils, n'oublie pas mon enseignement, mais que ton cœur garde mes commandements,
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
car ils vous ajouteront la durée des jours, années de vie, et de paix.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Ne laissez pas la bonté et la vérité vous abandonner. Attachez-les autour de votre cou. Écris-les sur la tablette de ton cœur.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Ainsi, vous trouverez la faveur, et une bonne compréhension aux yeux de Dieu et des hommes.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Fais confiance à Yahvé de tout ton cœur, et ne vous appuyez pas sur votre propre compréhension.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Dans toutes tes voies, reconnais-le, et il rendra vos chemins droits.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Ne sois pas sage à tes propres yeux. Craignez Yahvé, et éloignez-vous du mal.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Il sera sain pour votre corps, et de la nourriture pour vos os.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honorez Yahvé par vos biens, avec les prémices de toute votre production;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
ainsi vos granges seront remplies d'abondance, et vos cuves déborderont de vin nouveau.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mon fils, ne méprise pas la discipline de Yahvé, et ne vous lassez pas de sa correction;
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
car celui que Yahvé aime, il le corrige, comme un père reprend le fils dont il se réjouit.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Heureux l'homme qui trouve la sagesse, l'homme qui comprend.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Pour elle, un bon profit vaut mieux que de l'argent, et son retour est meilleur que l'or fin.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Elle est plus précieuse que les rubis. Aucune des choses que vous pouvez désirer ne doit être comparée à elle.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
La longueur des jours est dans sa main droite. Dans sa main gauche se trouvent les richesses et l'honneur.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Ses voies sont des voies agréables. Tous ses chemins sont la paix.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Elle est un arbre de vie pour ceux qui la saisissent. Heureux tous ceux qui la retiennent.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
C'est par la sagesse que Yahvé a fondé la terre. Par l'intelligence, il a établi les cieux.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Par sa connaissance, les profondeurs ont été brisées, et les cieux laissent tomber la rosée.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mon fils, qu'ils ne s'éloignent pas de tes yeux. Gardez la sagesse et la discrétion,
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
ainsi ils seront la vie de ton âme, et la grâce pour votre cou.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Alors tu marcheras dans ta voie en toute sécurité. Votre pied ne trébuchera pas.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Quand tu te coucheras, tu n'auras pas peur. Oui, tu te coucheras, et ton sommeil sera doux.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Ne craignez pas la peur soudaine, ni de la désolation des méchants, quand elle viendra;
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
car Yahvé sera ton assurance, et empêchera votre pied d'être pris.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Ne refusez pas le bien à ceux à qui il est dû, quand il est dans le pouvoir de votre main de le faire.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Ne dis pas à ton prochain: « Va, et reviens; demain je te le donnerai, » quand vous l'avez près de vous.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Ne médite pas le mal contre ton prochain, puisqu'il habite en sécurité près de vous.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Ne vous disputez pas avec un homme sans raison, s'il ne vous a fait aucun mal.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
N'enviez pas l'homme de violence. Ne choisissez aucune de ses voies.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Car le pervers est une abomination pour Yahvé, mais son amitié est avec les honnêtes gens.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
La malédiction de Yahvé est dans la maison des méchants, mais il bénit la demeure des justes.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Certes, il se moque des moqueurs, mais il donne la grâce aux humbles.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Les sages hériteront de la gloire, mais la honte sera la promotion des imbéciles.