< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
My son! my law forget not, And my commands let thy heart keep,
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
For length of days and years, Life and peace they do add to thee.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Let not kindness and truth forsake thee, Bind them on thy neck, Write them on the tablet of thy heart,
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
And find grace and good understanding In the eyes of God and man.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Trust unto Jehovah with all thy heart, And unto thine own understanding lean not.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
In all thy ways know thou Him, And He doth make straight thy paths.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Be not wise in thine own eyes, Fear Jehovah, and turn aside from evil.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Healing it is to thy navel, And moistening to thy bones.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honour Jehovah from thy substance, And from the beginning of all thine increase;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
And filled are thy barns [with] plenty, And [with] new wine thy presses break forth.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Chastisement of Jehovah, my son, despise not, And be not vexed with His reproof,
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
For whom Jehovah loveth He reproveth, Even as a father the son He is pleased with.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
O the happiness of a man [who] hath found wisdom, And of a man [who] bringeth forth understanding.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
For better [is] her merchandise Than the merchandise of silver, And than gold — her increase.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Precious she [is] above rubies, And all thy pleasures are not comparable to her.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Length of days [is] in her right hand, In her left [are] wealth and honour.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Her ways [are] ways of pleasantness, And all her paths [are] peace.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
A tree of life she [is] to those laying hold on her, And whoso is retaining her [is] happy.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Jehovah by wisdom did found the earth, He prepared the heavens by understanding.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
By His knowledge depths have been rent, And clouds do drop dew.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
My son! let them not turn from thine eyes, Keep thou wisdom and thoughtfulness,
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
And they are life to thy soul, and grace to thy neck.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Then thou goest thy way confidently, And thy foot doth not stumble.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
If thou liest down, thou art not afraid, Yea, thou hast lain down, And sweet hath been thy sleep.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Be not afraid of sudden fear, And of the desolation of the wicked when it cometh.
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
For Jehovah is at thy side, And He hath kept thy foot from capture.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Withhold not good from its owners, When thy hand [is] toward God to do [it].
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Say not thou to thy friend, 'Go, and return, and to-morrow I give,' And substance with thee.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Devise not against thy neighbour evil, And he sitting confidently with thee.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Strive not with a man without cause, If he have not done thee evil.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Be not envious of a man of violence, Nor fix thou on any of his ways.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
For an abomination to Jehovah [is] the perverted, And with the upright [is] His secret counsel.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
The curse of Jehovah [is] in the house of the wicked. And the habitation of the righteous He blesseth.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
If the scorners He doth scorn, Yet to the humble He doth give grace.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Honour do the wise inherit, And fools are bearing away shame!

< Karin Magana 3 >