< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
My son, forget not my law; but let thine heart keep my commandments:
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
For length of days, and years of life, and peace, shall they add to thee.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Let not mercy and truth forsake thee: bind them about thy neck; write them upon the table of thine heart:
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
So shalt thou find favour and good understanding in the sight of God and man.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Trust in the LORD with all thine heart, and lean not upon thine own understanding:
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
In all thy ways acknowledge him, and he shall direct thy paths.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Be not wise in thine own eyes; fear the LORD, and depart from evil:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
It shall be health to thy navel, and marrow to thy bones.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Honour the LORD with thy substance, and with the firstfruits of all thine increase:
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
So shall thy barns be filled with plenty, and thy vats shall overflow with new wine.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
My son, despise not the chastening of the LORD; neither be weary of his reproof:
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
For whom the LORD loveth he reproveth; even as a father the son in whom he delighteth.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Happy is the man that findeth wisdom, and the man that getteth understanding.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
For the merchandise of it is better than the merchandise of silver, and the gain thereof than fine gold.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
She is more precious than rubies: and none of the things thou canst desire are to be compared unto her.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Length of days is in her right had; in her left hand are riches and honour.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Her ways are ways of pleasantness, and all her paths are peace.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
She is a tree of life to them that lay hold upon her: and happy is every one that retaineth her.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
The LORD by wisdom founded the earth; by understanding he established the heavens.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
By his knowledge the depths were broken up, and the skies drop down the dew.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
My son, let not them depart from thine eyes; keep sound wisdom and discretion;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
So shall they be life unto thy soul, and grace to thy neck.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Then shalt thou walk in thy way securely, and thy foot shall not stumble.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
When thou liest down, thou shalt not be afraid: yea, thou shalt lie down, and thy sleep shall be sweet.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Be not afraid of sudden fear, neither of the desolation of the wicked, when it cometh:
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
For the LORD shall be thy confidence, and shall keep thy foot from being taken.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Withhold not good from them to whom it is due, when it is in the power of thine hand to do it.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Say not unto thy neighbour, Go, and come again, and tomorrow I will give; when thou hast it by thee.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Devise not evil against thy neighbour, seeing he dwelleth securely by thee.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Strive not with a man without cause, if he have done thee no harm.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Envy thou not the man of violence, and choose none of his ways.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
For the perverse is an abomination to the LORD: but his secret is with the upright.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
The curse of the LORD is in the house of the wicked; but he blesseth the habitation of the righteous.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Surely he scorneth the scorners, but he giveth grace unto the lowly.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
The wise shall inherit glory; but shame shall be the promotion of fools.