< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
My son, keep my teaching in your memory, and my rules in your heart:
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
For they will give you increase of days, years of life, and peace.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Let not mercy and good faith go from you; let them be hanging round your neck, recorded on your heart;
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
So you will have grace and a good name in the eyes of God and men.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Put all your hope in God, not looking to your reason for support.
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
In all your ways give ear to him, and he will make straight your footsteps.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Put no high value on your wisdom: let the fear of the Lord be before you, and keep yourself from evil:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
This will give strength to your flesh, and new life to your bones.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Give honour to the Lord with your wealth, and with the first-fruits of all your increase:
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
So your store-houses will be full of grain, and your vessels overflowing with new wine.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
My son, do not make your heart hard against the Lord's teaching; do not be made angry by his training:
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
For to those who are dear to him the Lord says sharp words, and makes the son in whom he has delight undergo pain.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Happy is the man who makes discovery of wisdom, and he who gets knowledge.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
For trading in it is better than trading in silver, and its profit greater than bright gold.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
She is of more value than jewels, and nothing for which you may have a desire is fair in comparison with her.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Long life is in her right hand, and in her left are wealth and honour.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Her ways are ways of delight, and all her goings are peace.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
She is a tree of life to all who take her in their hands, and happy is everyone who keeps her.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
The Lord by wisdom put in position the bases of the earth; by reason he put the heavens in their place.
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
By his knowledge the deep was parted, and dew came dropping from the skies.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
My son, keep good sense, and do not let wise purpose go from your eyes.
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
So they will be life for your soul, and grace for your neck.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Then you will go safely on your way, and your feet will have no cause for slipping.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
When you take your rest you will have no fear, and on your bed sleep will be sweet to you.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Have no fear of sudden danger, or of the storm which will come on evil-doers:
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
For the Lord will be your hope, and will keep your foot from being taken in the net.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Do not keep back good from those who have a right to it, when it is in the power of your hand to do it.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Say not to your neighbour, Go, and come again, and tomorrow I will give; when you have it by you at the time.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Do not make evil designs against your neighbour, when he is living with you without fear.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Do not take up a cause at law against a man for nothing, if he has done you no wrong.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Have no envy of the violent man, or take any of his ways as an example.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
For the wrong-hearted man is hated by the Lord, but he is a friend to the upright.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
The curse of the Lord is on the house of the evil-doer, but his blessing is on the tent of the upright.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
He makes sport of the men of pride, but he gives grace to the gentle-hearted.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
The wise will have glory for their heritage, but shame will be the reward of the foolish.