< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Mijn zoon, vergeet mijn onderricht niet, Neem mijn wenken ter harte.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Ze schenken u lengte van dagen, jaren van leven, En overvloedige welvaart!
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Liefde en trouw mogen u nimmer verlaten, Hang ze om uw hals, schrijf ze op de tafel van uw hart;
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Dan zult ge goed en verstandig zijn, In de ogen van God en de mensen.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Vertrouw op Jahweh met heel uw hart, Verlaat u niet op uw eigen inzicht;
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Denk aan Hem op al uw wegen, Dan zal Hij uw paden effenen.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Wees niet wijs in uw eigen ogen, Heb ontzag voor Jahweh en vermijd het kwaad:
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Het zal genezing brengen voor uw lichaam, Verkwikking voor uw gebeente.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Eer Jahweh met heel uw bezit, Met het beste van al uw inkomsten:
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
Dan zullen uw schuren vol koren zijn, Uw kuipen bersten van most.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Mijn zoon, sla de lessen van Jahweh niet in de wind, Heb geen afkeer van zijn bestraffing;
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Want Jahweh tuchtigt hem, dien Hij liefheeft, Kastijdt het kind, dat Hij mag.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Gelukkig de mens, die wijsheid verkreeg, De man die inzicht bekwam;
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Want haar voordelen zijn groter dan die van zilver, Wat zij opbrengt is beter dan goud.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Zij is meer waard dan juwelen; Geen van uw kostbaarheden komt haar nabij!
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Met de rechterhand schenkt ze lengte van dagen, Met de linker rijkdom en aanzien.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
Haar wegen zijn liefelijke wegen, Al haar paden leiden tot vrede;
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Zij is een boom des levens voor wie haar vatten, En wie haar vasthoudt, is zalig te prijzen!
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Met wijsheid heeft Jahweh de aarde gegrond, Met inzicht de hemel gewelfd;
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
Naar zijn kennis rollen de zeeën aan, En druppelen de wolken van dauw.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Mijn zoon, verlies ze dus niet uit het oog, Maar doe alles met beleid en verstand;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Laat ze het leven zijn voor uw ziel, Een sieraad voor uw hals.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Dan zult ge veilig uw weg bewandelen, En zult ge uw voeten niet stoten;
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Dan behoeft ge niet te vrezen, als ge u neerlegt, Kunt ge rustig sluimeren, als ge wilt slapen.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Dan behoeft ge niet te vrezen, voor wat de dommen verschrikt, Of als het onweer komt, dat de bozen overvalt;
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Want Jahweh zal zijn op al uw wegen, Uw voet behoeden voor de strik.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Weiger het goede niet, aan wien het toekomt, Zolang het in uw macht is, het te doen.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Zeg niet tot uw naaste: "Ga heen en kom nog eens terug"; Of "Mórgen krijgt ge iets", terwijl ge het nú hebt!
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Smeed geen kwaad tegen uw naaste, Terwijl hij, niets duchtend, bij u verblijft;
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Zoek geen twist met iemand om niets, Als hij u geen kwaad heeft gedaan.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Wees niet jaloers op een tyran, Laat geen zijner wegen u gevallen;
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Want Jahweh heeft een afschuw van den zondaar, Maar met de rechtvaardigen gaat Hij vertrouwelijk om.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
De vloek van Jahweh rust op het huis van den boze, Zijn zegen op de woning der rechtvaardigen;
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Met spotters drijft Hij de spot, Maar aan de nederigen schenkt hij genade.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Wijzen zullen achting verwerven, Dwazen schande verkrijgen!

< Karin Magana 3 >