< Karin Magana 3 >
1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Min Søn, glem ikke, hvad jeg har lært dig, dit Hjerte tage vare paa mine Bud!
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Thi en Række af Dage og Leveaar og Lykke bringer de dig.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Godhed og Troskab vige ej fra dig, bind dem som Baand om din Hals, skriv dem paa dit Hjertes Tavle!
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Saa finder du Naade og Yndest i Guds og Menneskers Øjne.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Stol paa HERREN af hele dit Hjerte, men forlad dig ikke paa din Forstand;
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
hav ham i Tanke paa alle dine Veje, saa jævner han dine Stier.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Hold ikke dig selv for viis, frygt HERREN og vig fra det onde;
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
saa faar du Helse for Legemet, Lindring for dine Ledemod.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Ær med din Velstand HERREN med Førstegrøden af al din Avl;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
da fyldes dine Lader med Korn, dine Perser svømmer over af Most.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Min Søn, lad ej haant om HERRENS Tugt, vær ikke ked af hans Revselse;
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
HERREN revser den, han elsker, han straffer den Søn, han har kær.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Lykkelig den, der har opnaaet Visdom, den, der vinder sig Indsigt;
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
thi den er bedre at købe end Sølv, bedre at vinde end Guld;
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
den er mere værd end Perler, ingen Klenodier opvejer den;
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
en Række af Dage er i dens højre, i dens venstre Rigdom og Ære;
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
dens Veje er liflige Veje, og alle dens Stier er Lykke;
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
den er et Livets Træ for dem, der griber den, lykkelig den, som holder den fast!
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
HERREN grundlagde Jorden med Visdom, grundfæsted Himlen med Indsigt;
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
ved hans Kundskab brød Strømmene frem, lader Skyerne Dug dryppe ned.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Min Søn, tag Vare paa Snilde og Kløgt, de slippe dig ikke af Syne;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
saa bliver de Liv for din Sjæl og et yndigt Smykke til din Hals.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Da vandrer du trygt din Vej, støder ikke imod med din Fod;
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
sætter du dig, skal du ikke skræmmes, lægger du dig, skal din Søvn vorde sød;
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
du skal ikke frygte uventet Rædsel, Uvejret, naar det kommer over gudløse;
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
thi HERREN skal være din Tillid, han vogter din Fod, saa den ikke hildes.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Nægt ikke den trængende Hjælp, naar det staar i din Magt at hjælpe;
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
sig ej til din Næste: »Gaa og kom igen, jeg vil give i Morgen!« — saafremt du har det.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Tænk ikke paa ondt mod din Næste, naar han tillidsfuldt bor i din Nærhed.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Yp ikke Trætte med sagesløs Mand, naar han ikke har voldet dig Men.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Misund ikke en Voldsmand, græm dig aldrig over hans Veje;
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
thi den falske er HERREN en Gru; mod retsindig er han fortrolig;
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
i den gudløses Hus er HERRENS Forbandelse, men retfærdiges Bolig velsigner han.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Over for Spottere bruger han Spot, men ydmyge giver han Naade.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
De vise faar Ære til Arv, men Taaber høster kun Skam.