< Karin Magana 3 >

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
Ka capa, kak awipek ve koeh hilh nawh, nak kawlung awh kym lah.
2 gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
Na hqingnaak khawnghii khawkum ingkaw ngaiqeepnaakkhqi ing ni tawmsap kaw.
3 Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
Qeennaak ingkaw awitak ing nang ce koeh ni hooet seh.
4 Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
Cawhtaw, Khawsa ingkaw thlanghqing mik huh awh mikhaileek ingkaw mingleeknaak ce pang kawp ti.
5 Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
Nak kawlung boeih ing Bawipa ce caang na nawh, Na siimnaak awh koeh hang qu;
6 cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
Na lam hoeiawh amah ce siim poe nawh, na lam ce nim huh kaw.
7 Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
Namah ngaih awh ak cyina koeh ngai qu nawh; Bawipa ce kqih nawh, thawlhnaak ce cehtaak.
8 Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
Nak thangqui ham sadingnaak na awm nawh, na quh ham ak thlikna awm kaw.
9 Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
Na khawhkham ing Khawsa ce kyihcah lah. Na them ak pung law lammacyk boeih ing awm;
10 ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
Cawhtaw nak khai baawp ing bee ngen kawm saw, na misur um ing bee poeng kaw.
11 Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
Ka capa, Bawipa a toelnaak ce koeh husit nawh, A ni toelzyihnaak ce koeh zadam kawp ti.
12 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
Bawipa ing a lungnak cekhqi ce toel khawi nawh, Pa ing ca a lungnak awh a toelzyih khawi a myihna.
13 Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
Cyihnaak ak hu ak thlang ingkaw kawcyihnaak ak hu ak thlang taw a zoseen hy.
14 gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
Cetaw ngun a phu tlo ingkaw sui a phu tlo ang lakawh a phu tlo ngai hy.
15 Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
Suilung a phu tlo lakawh a phu tlo ngai nawh ngaihnaak ing awm am pha thai hy.
16 Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
Ak tangkut benawh hqinglung sangnaak awm nawh, ak cawngkut benawh khawhthem ingkaw boeimangnaak ce awm hy.
17 Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
A lam ce awmhlynaak lampyina awm nawh, a lam boeihboeih ce ngaiqeepnaak ing bee hy.
18 Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
Ak tuu thlang boeih ham hqingnaak thingkungna awm nawh, ak kym thlang boeih ham zoseennaak ni.
19 Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
Bawipa ing a cyihnaak ing khawmdek ve syyn nawh, ak kawcyih ing khan ce caksak hy;
20 ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
A thoemnaak ing tuinu ce hqaa sak nawh, cingmai ing daamtui baw sak hy.
21 Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
Ka capa, na mik ing khaw koeh hang seh, cyihnaak ingkaw khawkpoek thainaak ce ak cakna tu;
22 za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
Na hqingnaak ham hqingnaakna awm nawh, na haawng ham mikhaileek na awm kaw.
23 Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
Cawhce na lamawh ak dingna cet kawm tik saw, na khaw am tawngtawh kaw.
24 sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
Na ih awm am kqih kawm tik saw, nang zaih nawh na ih awhawm na ih tui kaw.
25 Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
Kqihlyynaak bawtbet awh ak dang law ce koeh kqih nawh, thlang ak mukkhqi a pha law awhawm koeh kqih kawp ti.
26 gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Bawipa taw na loetnaak na awm nawh, na khaw thang awhkawng ni doen kaw.
27 Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
Themleek ak hu tyngkhqi a do hly kawi themleek koeh haimah, na kutawh dangsak ham na taak khui taw.
28 Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
Na imceng venawh, “Ceh nawh ak changna va sui cang nawh voei law tlaih khawngawi ni pe kawng nyng,” koeh ti, na taak a loeiawh.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
Na imceng ak khanawh khawboeseet koeh toen, ni yp na nawh na venawh khawksa ni ti na sim loei.
30 Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
Khawboeseetnaak nak khanawh a ma toen awhtaw leehcaihnaak a awm kaana na kut koeh thlak.
31 Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
Khawboeseet ak toen ak thlang koeh ooet nawh a lampyi awh koeh hquut.
32 Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
Ak thymna khaw amak sa taw Bawipa mikhuh awh tyih kawina awm nawh thlakleekkhqi taw pyi nak khqi hy.
33 La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
Bawipa a khawsii taw thlakche khqi imawh awm nawh, thlakdyng khqi cunnaak taw zoseenaak ing bee hy.
34 Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
Thlang ak husitkhqi ce husitkhqi nawh, kawkneemkhqi ce qeennaak ham sak khqi hy.
35 Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
Kyihcahnaak taw thlakcyi ing ham nawh chahpyihnaak taw thlakqaw ing ham kaw.

< Karin Magana 3 >