< Karin Magana 29 >

1 Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shi ba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
Un homme souvent réprimandé et persistant dans son entêtement est brisé soudain et sans retour.
2 Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
Quand dominent les justes, le peuple est en joie; quand les méchants gouvernent, le peuple gémit.
3 Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki, amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
L’Homme qui aime la sagesse réjouit son père; celui qui fréquente des courtisanes mange son bien.
4 Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
Un roi grandit son pays par la justice: avide de dons, il le ruine.
5 Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
Qui flatte son prochain tend un filet sous ses pas.
6 Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa, amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
Le péché devient un piège pour le méchant; le juste jubile et savoure sa joie.
7 Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa, amma mugaye ba su da wannan damuwa.
Le juste se pénètre du droit des humbles; le méchant ne sait rien comprendre.
8 Masu ba’a kan kuta faɗa a birni, amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
Les persifleurs mettent la ville en ébullition; les sages apaisent les colères.
9 In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa, wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
Quand un sage est en discussion avec un sot, celui-ci s’emporte ou ricane, mais de calme, point!
10 Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
Les assassins en veulent à l’innocent; les honnêtes gens recherchent sa personne.
11 Wawa yakan nuna fushinsa a fili, amma mai hikima kan kanne fushinsa.
Le sot lâche toute sa mauvaise humeur; le sage finit par la calmer.
12 In mai mulki yana sauraran ƙarairayi, dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
Le souverain accueille-t-il le mensonge, tous ses serviteurs sont pervers.
13 Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya. Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
Le pauvre et l’exploiteur se retrouvent ensemble: l’Eternel fait luire sa lumière aux yeux de tous deux.
14 In sarki yana hukunta talakawa da adalci kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
Que le roi juge les humbles avec équité, son trône en sera affermi à jamais.
15 Sandar gyara kan ba da hikima, amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
Verge et reproches inculquent la sagesse, un enfant livré à lui-même fait le déshonneur de sa mère.
16 Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa, amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
Quand les méchants dominent, le mal augmente, mais les justes seront témoins de leur chute.
17 Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama; zai ba ka farin cikin da kake so.
Corrige ton fils, tu en auras du plaisir; il donnera de douces joies à ton âme.
18 Inda ba wahayi, mutane kan kangare; amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
Faute de, révélation prophétique, le peuple s’abandonne au désordre; mais heureux s’il observe la loi!
19 Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai; ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
Ce n’est pas avec des paroles qu’on corrige l’esclave: s’il les comprend, il n’en tient pas compte.
20 Ka ga mutum mai yin magana da garaje? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
Vois-tu un homme précipité dans ses paroles, le sot a plus d’avenir que lui.
21 In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro, zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
Qui gâte son esclave dès l’enfance aboutit à en faire un parasite.
22 Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa, mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
Un homme irascible provoque des disputes; qui se laisse emporter par la colère accumule les fautes.
23 Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
L’Orgueil de l’homme amène son abaissement; la modestie est une source d’honneur.
24 Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne; yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
Qui partage avec un voleur est son propre ennemi: il entend l’adjuration et ne peut rien dénoncer.
25 Jin tsoron mutum tarko ne, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
La peur fait tomber l’homme dans un piège; qui met sa confiance en l’Eternel est à l’abri.
26 Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki, amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
Beaucoup recherchent la faveur du prince; mais c’est Dieu qui attribue à chacun son dû.
27 Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya; mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.
Le malfaiteur est en horreur aux justes, et l’honnête homme est en horreur au méchant.

< Karin Magana 29 >