< Karin Magana 29 >

1 Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shi ba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
A man that, having received many admonitions, still hardeneth his neck, will suddenly be broken, and this without remedy.
2 Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
When the righteous are in authority, the people will rejoice; but when the wicked beareth rule, the people groan.
3 Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki, amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
The man that loveth wisdom causeth his father to rejoice; but he that keepeth company with harlots wasteth [his] wealth.
4 Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
A king will through the exercise of justice establish [the welfare of] a land; but one that loveth gifts overthroweth it.
5 Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
A man that flattereth his neighbor spreadeth a net for his steps.
6 Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa, amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
In the transgression of a man there is an evil snare: but the righteous ever singeth and rejoiceth.
7 Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa, amma mugaye ba su da wannan damuwa.
The righteous considereth the cause of the indigent: but the wicked will not understand the knowledge [of justice].
8 Masu ba’a kan kuta faɗa a birni, amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
Scornful men will kindle [confusion] in a town; but the wise turn away wrath.
9 In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa, wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
If a wise man contend with a foolish man, whether he be angry or whether he laugh, [he will have] no rest.
10 Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
Men of blood hate the guiltless one; but the upright seek [to preserve] his life.
11 Wawa yakan nuna fushinsa a fili, amma mai hikima kan kanne fushinsa.
A fool uttereth all his mind; but the wise holdeth it back.
12 In mai mulki yana sauraran ƙarairayi, dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
If a ruler listen to the word of falsehood, all his servants become wicked.
13 Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya. Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
The poor and the man of exactions meet together: the Lord enlighteneth the eyes of both of them.
14 In sarki yana hukunta talakawa da adalci kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
When a king judgeth in truth the indigent, his throne shall stand firmly for ever.
15 Sandar gyara kan ba da hikima, amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
The rod and reproof impart wisdom; but a lad abandoned to himself bringeth shame on his mother.
16 Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa, amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
With the increase of the wicked transgression increaseth; but the righteous shall yet look on their downfall.
17 Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama; zai ba ka farin cikin da kake so.
Correct thy son, and he will procure thee rest: yea, he will give delight unto thy soul.
18 Inda ba wahayi, mutane kan kangare; amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
Without a prophetic vision a people become unruly; but when it observeth the law, then will it be happy.
19 Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai; ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
Not with words [alone] can a servant be corrected; for though he understand, there will be no response.
20 Ka ga mutum mai yin magana da garaje? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
Seest then a man that is hasty in his words? there is more hope for a fool than for him.
21 In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro, zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
If one rear his servant delicately from his youth, then will he at length become as [his] son.
22 Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa, mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
A man of anger stirreth up strife; and a man of fury aboundeth in transgression.
23 Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
The pride of a man will humble him; but the humble in spirit will attain to honor.
24 Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne; yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
Whoso divideth with a thief hateth his own soul: he heareth the adjuration and dareth not to tell.
25 Jin tsoron mutum tarko ne, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
The dread of man bringeth a snare; but whoso putteth his trust in the Lord will be upheld in safety.
26 Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki, amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
Many seek the favor of a ruler; but from the Lord cometh justice for man.
27 Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya; mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.
An abomination of the righteous is an unjust man: and an abomination of the wicked is one who is upright in [his] way.

< Karin Magana 29 >