< Karin Magana 29 >

1 Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shi ba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
He, that being often reproved hardeneth [his] neck, shall suddenly be destroyed, and that without remedy.
2 Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
When the righteous are in authority, the people rejoice: but when the wicked beareth rule, the people mourn.
3 Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki, amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
Whoso loveth wisdom rejoiceth his father: but he that keepeth company with harlots spendeth [his] substance.
4 Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
The king by judgment establisheth the land: but he that receiveth gifts overthroweth it.
5 Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
A man that flattereth his neighbour spreadeth a net for his feet.
6 Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa, amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
In the transgression of an evil man [there is] a snare: but the righteous doth sing and rejoice.
7 Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa, amma mugaye ba su da wannan damuwa.
The righteous considereth the cause of the poor: [but] the wicked regardeth not to know [it].
8 Masu ba’a kan kuta faɗa a birni, amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
Scornful men bring a city into a snare: but wise [men] turn away wrath.
9 In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa, wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
[If] a wise man contendeth with a foolish man, whether he rage or laugh, [there is] no rest.
10 Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
The bloodthirsty hate the upright: but the just seek his soul.
11 Wawa yakan nuna fushinsa a fili, amma mai hikima kan kanne fushinsa.
A fool uttereth all his mind: but a wise [man] keepeth it in till afterwards.
12 In mai mulki yana sauraran ƙarairayi, dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
If a ruler hearken to lies, all his servants [are] wicked.
13 Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya. Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
The poor and the deceitful man meet together: the LORD lighteneth both their eyes.
14 In sarki yana hukunta talakawa da adalci kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
The king that faithfully judgeth the poor, his throne shall be established for ever.
15 Sandar gyara kan ba da hikima, amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
The rod and reproof give wisdom: but a child left [to himself] bringeth his mother to shame.
16 Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa, amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
When the wicked are multiplied, transgression increaseth: but the righteous shall see their fall.
17 Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama; zai ba ka farin cikin da kake so.
Correct thy son, and he shall give thee rest; yea, he shall give delight unto thy soul.
18 Inda ba wahayi, mutane kan kangare; amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
Where [there is] no vision, the people perish: but he that keepeth the law, happy [is] he.
19 Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai; ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
A servant will not be corrected by words: for though he understand he will not answer.
20 Ka ga mutum mai yin magana da garaje? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
Seest thou a man [that is] hasty in his words? [there is] more hope of a fool than of him.
21 In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro, zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
He that delicately bringeth up his servant from a child shall have him become [his] son at the length.
22 Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa, mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
An angry man stirreth up strife, and a furious man aboundeth in transgression.
23 Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
A man’s pride shall bring him low: but honour shall uphold the humble in spirit.
24 Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne; yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
Whoso is partner with a thief hateth his own soul: he heareth cursing, and bewrayeth [it] not.
25 Jin tsoron mutum tarko ne, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
The fear of man bringeth a snare: but whoso putteth his trust in the LORD shall be safe.
26 Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki, amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
Many seek the ruler’s favour; but [every] man’s judgment [cometh] from the LORD.
27 Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya; mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.
An unjust man [is] an abomination to the just: and [he that is] upright in the way [is] abomination to the wicked.

< Karin Magana 29 >