< Karin Magana 29 >
1 Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shi ba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
Ngʼat masiko katoke tek bangʼ siem mangʼeny ibiro tieko apoya nono maonge konyruok.
2 Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
Ka joma kare dhiyo nyime, ji mor, ka joricho ema otelo e loch ji ywak ka gichur.
3 Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki, amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
Ngʼat mohero rieko miyo wuon mare mor, to ngʼat momako osiep kod jachode ketho mwandune.
4 Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
Gi adiera ema ruoth miyo piny bet mochungʼ motegno, to ngʼat mawuor ne asoya muke magoye piny.
5 Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
Ngʼat mawuondo jabute ochiko obadho e tiende.
6 Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa, amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
Ngʼat marach dwodore e obadho mar richone owuon, to ngʼat makare nyalo wer mobed mamor.
7 Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa, amma mugaye ba su da wannan damuwa.
Ngʼat makare winjo ywak jochan mondo otimnegi gima kare, to ngʼat marach ok dew gimoro.
8 Masu ba’a kan kuta faɗa a birni, amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
Joma jaro ji kelo koko e dala, to jomariek ringo aa e mirima.
9 In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa, wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
Ka ngʼat mariek odhiyo gi ngʼat mofuwo e od bura, to ngʼat mofuwo goyo koko kendo jero, kendo kwe bedo maonge.
10 Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
Joma ohero chwero remo mon kod jogo modimbore, kendo gidwaro yo mar nego joma jo-ratiro.
11 Wawa yakan nuna fushinsa a fili, amma mai hikima kan kanne fushinsa.
Ngʼat mofuwo chiwore duto komwomore amwoma e mirimbe, to ngʼat mariek ritore ka ogare.
12 In mai mulki yana sauraran ƙarairayi, dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
Ka ruoth thoro chiko ite ne miriambo, to jootene duto bedo joma timbegi richo.
13 Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya. Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
Jachan gi ngʼat mahinyo ji nigi gimoro achiel machalre: Jehova Nyasaye miyogi wenge maneno kargi ji ariyogo.
14 In sarki yana hukunta talakawa da adalci kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
Ka ruoth ongʼado bura ne jochan kod adiera, kom ruodhe biro bedo moritore ma ok hinyre.
15 Sandar gyara kan ba da hikima, amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
Ka ichwado nyathi kendo ikwere eka ikonye bedo mariek to nyathi ma owe aweya kelo wichkuot ne min mare.
16 Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa, amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
Ka jaricho dhiyo nyime maber, e kaka richo bende medore, to joma kare biro neno podho margi.
17 Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama; zai ba ka farin cikin da kake so.
Kum wuodi, to obiro miyi kwe; kendo obiro kelo mor ne chunyi.
18 Inda ba wahayi, mutane kan kangare; amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
Kama onge lek, to ji chunygi aa to ngʼama orito chik en ngʼat mogwedhi.
19 Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai; ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
Misumba ok nyal kony kirieye mana gi wach kende; kata bed ni owinjo, to ok obi rwako.
20 Ka ga mutum mai yin magana da garaje? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
Bende ineno ngʼato ma wuoyo ka rikni mapiyo piyo? Nitie geno mathoth kuom ngʼat mofuwo maloye.
21 In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro, zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
Ka ngʼato omiyo misumbane gik moko duto chakre ka en rawera, obiro kelo kuyo e gikone.
22 Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa, mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
Ngʼat ma iye owangʼ kelo masira, to ngʼat makecho piyo timo richo mathoth.
23 Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
Sunga ngʼato ema miyo opodho, to ngʼat ma chunye muol yudo pak.
24 Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne; yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
Ngʼat makonyo jakuo mondo okwal ema bedo jasike owuon; nikech osekwongʼore kendo ok onyal bedo janeno.
25 Jin tsoron mutum tarko ne, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
Luoro mar dhano biro nyisore ni en gima duodo ngʼato, to ngʼat mogeno kuom Jehova Nyasaye orite maonge hinyruok.
26 Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki, amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
Ji mangʼeny dwaro mondo girom gi ruoth, to en mana kuom Jehova Nyasaye ema adiera yudoree.
27 Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya; mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.
Joma kare mon gi joma ok jo-adiera, to joricho mon gi joma oriere tir.