< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Niegodziwi uciekają, choć nikt ich nie goni, ale sprawiedliwi są dzielni jak lew.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
Z powodu grzechu ziemi wielu [jest] jej władców, ale dzięki człowiekowi roztropnemu i rozumnemu będzie trwała.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
Ubogi człowiek, który gnębi biednych, [jest jak] gwałtowny deszcz, po którym nie ma chleba.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Ci, którzy odstępują od prawa, chwalą niegodziwych, lecz ci, którzy przestrzegają prawa, zwalczają ich.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Źli ludzie nie rozumieją sądu, ale ci, którzy szukają PANA, rozumieją wszystko.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Lepszy jest ubogi, który postępuje uczciwie, niż człowiek przewrotny w [swych] drogach, chociaż jest bogaty.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Kto przestrzega prawa, jest rozumnym synem, a towarzysz rozwiązłych hańbi swego ojca.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
Kto pomnaża swój majątek lichwą i odsetkami, zbiera go dla tego, kto zlituje się nad ubogimi.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
Kto odwraca swe ucho, aby nie słyszeć prawa, nawet jego modlitwa budzi odrazę.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Kto sprowadza prawych na złą drogę, sam wpadnie we własny dół, ale nienaganni odziedziczą dobro.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
Bogacz jest mądry w swoich oczach, ale rozumny biedak go bada.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Gdy sprawiedliwi się radują, jest wielka chwała, a gdy niegodziwi powstają, człowiek się kryje.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
Kto ukrywa swe grzechy, nie będzie miał szczęścia, ale kto [je] wyznaje i porzuca, dostąpi miłosierdzia.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Błogosławiony człowiek, który się zawsze boi, ale kto zatwardza swoje serce, wpada w nieszczęście.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Jak lew ryczący i zgłodniały niedźwiedź, tak niegodziwy władca panujący nad ubogim ludem.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Władca bezrozumny jest wielkim ciemięzcą, [a] kto nienawidzi chciwości, przedłuży swoje dni.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
Człowiek, który przeleje krew ludzką, ucieknie aż do dołu; [niech] nikt go nie zatrzymuje.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Kto postępuje uczciwie, będzie wybawiony, a przewrotny na [swoich] drogach nagle upadnie.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
Kto uprawia swoją ziemię, nasyci się chlebem, a kto naśladuje próżniaków, nasyci się nędzą.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
Wierny człowiek będzie opływał w błogosławieństwa, a kto chce się szybko wzbogacić, nie będzie bez winy.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Niedobrze jest mieć wzgląd na osobę, bo dla kęsa chleba niejeden popełni przestępstwo.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
Kto chce szybko się wzbogacić, ma złe oko, a nie wie, że przyjdzie na niego bieda.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
Kto strofuje człowieka, znajdzie potem [więcej] przychylności niż ten, który pochlebia językiem.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Kto kradnie ojcu lub matce i mówi: To nie grzech, jest towarzyszem zbójcy.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
Człowiek wyniosły wszczyna spór, ale kto pokłada ufność w PANU, będzie nasycony.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
Kto ufa własnemu sercu, jest głupi, a kto mądrze postępuje, będzie ocalony.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
Kto daje ubogiemu, nie zazna braku, a [na tego], kto odwraca swe oczy [od niego], spadnie wiele przekleństw.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Gdy niegodziwi powstają, ludzie się kryją, ale gdy giną, sprawiedliwi się mnożą.

< Karin Magana 28 >