< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
تعاقب کننده‌ای نیست، اما عادلان مثل شیر شجاعند.۱
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
از معصیت اهل زمین حاکمانش بسیارمی شوند، اما مرد فهیم و دانا استقامتش برقرارخواهد ماند.۲
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
مرد رئیس که بر مسکینان ظلم می‌کند مثل باران است که سیلان کرده، خوراک باقی نگذارد.۳
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
هر‌که شریعت را ترک می‌کند شریران رامی ستاید، اما هر‌که شریعت را نگاه دارد از ایشان نفرت دارد.۴
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
مردمان شریر انصاف را درک نمی نمایند، اماطالبان خداوند همه‌چیز را می‌فهمند.۵
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
فقیری که در کاملیت خود سلوک نماید بهتراست از کج رونده دو راه اگر‌چه دولتمند باشد.۶
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
هر‌که شریعت را نگاه دارد پسری حکیم است، اما مصاحب مسرفان، پدر خویش را رسوامی سازد.۷
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
هر‌که مال خود را به ربا و سود بیفزاید، آن رابرای کسی‌که بر فقیران ترحم نماید، جمع می‌نماید.۸
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
هر‌که گوش خود را از شنیدن شریعت برگرداند، دعای او هم مکروه می‌شود.۹
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
هر‌که راستان را به راه بد گمراه کند به حفره خود خواهد افتاد، اما صالحان نصیب نیکوخواهند یافت.۱۰
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
مرد دولتمند در نظر خود حکیم است، امافقیر خردمند او را تفتیش خواهد نمود.۱۱
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
چون عادلان شادمان شوند فخر عظیم است، اما چون شریران برافراشته شوند مردمان خود را مخفی می‌سازند.۱۲
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
هر‌که گناه خود را بپوشاند برخوردارنخواهد شد، اما هر‌که آن را اعتراف کند و ترک نماید رحمت خواهد یافت.۱۳
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
خوشابحال کسی‌که دائم می‌ترسد، اما هرکه دل خود را سخت سازد به بلا گرفتار خواهدشد.۱۴
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
حاکم شریر بر قوم مسکین، مثل شیر غرنده و خرس گردنده است.۱۵
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
حاکم ناقص العقل بسیار ظلم می‌کند، اماهر‌که از رشوه نفرت کند عمر خود را درازخواهد ساخت.۱۶
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
کسی‌که متحمل بار خون شخصی شود، به هاویه می‌شتابد. زنهار کسی او را باز ندارد.۱۷
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
هر‌که به استقامت سلوک نماید رستگارخواهد شد، اما هر‌که در دو راه کج رو باشد دریکی از آنها خواهد افتاد.۱۸
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
هر‌که زمین خود را زرع نماید از نان سیرخواهد شد، اما هر‌که پیروی باطلان کند از فقرسیر خواهد شد.۱۹
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
مرد امین برکت بسیار خواهد یافت، اماآنکه در‌پی دولت می‌شتابد بی‌سزا نخواهد ماند.۲۰
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
طرفداری نیکو نیست، و به جهت لقمه‌ای نان، آدمی خطاکار می‌شود.۲۱
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
مرد تنگ نظر در‌پی دولت می‌شتابد ونمی داند که نیازمندی او را درخواهد یافت.۲۲
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
کسی‌که آدمی را تنبیه نماید، آخر شکرخواهد یافت، بیشتر از آنکه به زبان خودچاپلوسی می‌کند.۲۳
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
کسی‌که پدر و مادر خود را غارت نماید وگوید گناه نیست، مصاحب هلاک کنندگان خواهدشد.۲۴
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
مرد حریص نزاع را برمی انگیزاند، اما هر‌که بر خداوند توکل نماید قوی خواهد شد.۲۵
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
آنکه بر دل خود توکل نماید احمق می‌باشد، اما کسی‌که به حکمت سلوک نمایدنجات خواهد یافت.۲۶
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
هر‌که به فقرا بذل نماید محتاج نخواهدشد، اما آنکه چشمان خود را بپوشاند لعنت بسیارخواهد یافت.۲۷
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
وقتی که شریران برافراشته شوند مردم خویشتن را پنهان می‌کنند، اما چون ایشان هلاک شوند عادلان افزوده خواهند شد.۲۸

< Karin Magana 28 >