< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Umuntu omubi uyabaleka loba engaxotshaniswa muntu, kodwa abalungileyo balesibindi njengesilwane.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
Nxa ilizwe lihlamuka liba lababusi abanengi, kodwa umuntu ozwisisayo lololwazi ugcina ukuthula.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
Umbusi oncindezela abayanga unjengezulu elinengi elikhukhula amabele.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Labo abaphikisa umthetho bakhuthaza izigangi, kodwa labo abawugcinayo bayazenqabela.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Abantu ababi kabakuzwisisi ukwahlulela kuhle, kodwa labo abamdingayo uThixo bayakuzwisisa kakhulu.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Ungcono umyanga ohamba ngokulunga kulesinothi esilezindlela zokungcola.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Lowo ogcina umthetho yindodana eqedisisayo, kodwa umngane wezixhwali uyangisa uyise.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
Lowo owandisa inotho yakhe ngenzaliso uyibuthela omunye ozaba lomusa kubayanga.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
Loba ngubani ongawulaleliyo umthetho, lemikhuleko yakhe izakuba yisinengiso.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Lowo oholela olungileyo endleleni embi uzawela emjibileni wakhe, kodwa ongelacala uzakwamukela ilifa elihle.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
Umuntu onothileyo angazibona ingathi uhlakaniphile, kodwa umyanga oqedisisayo uhle abone ukuthi kasumuntu.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Nxa olungileyo enqoba kulokujabula okukhulu; kodwa nxa omubi ethatha umbuso abantu bayacatsha.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
Lowo ofihla iziphambeko zakhe kayikuphumelela, kodwa lowo ozivumayo azitshiye ufumana umusa.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Ubusisiwe umuntu ohlala emesaba uThixo, kodwa lowo oyenza lukhuni inhliziyo yakhe uwela enkathazweni.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Njengesilwane esibhongayo loba ibhele elihlaselayo unjalo umuntu omubi nxa ebusa abantu abangelamandla.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Umbusi oncindezelayo wehluleka ukwahlulela kuhle, kodwa lowo ozonda inzuzo yokuganga uzakuba lempilo ende.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
Umuntu odliwa ngumzwangedwa wokubulala omunye uzaba ngohlala ebaleka aze ayokufa; akungabi lomuntu omsekelayo.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Lowo ompilo yakhe ingelacala uvikelekile, kodwa ondlela zakhe zixhwalile uzakuwa masinyane.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
Lowo osebenza nzima emasimini akhe uzathola ukudla okunengi, kodwa lowo ophika ngezifiso eziyize uzakuba ngumyanga onukayo.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
Umuntu othembekileyo uzabusiswa ngokuphumelela, kodwa ogijimela ukunotha kayikuphepha ekujezisweni.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Ukubandlulula abantu kakulunganga ikanti umuntu uyona ukuze azuze ucezu lwesinkwa.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
Umuntu oncitshanayo utshisekela ukunotha kodwa kaboni ukuthi unyenyelwa yibuyanga.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
Lowo okhuza umuntu uzacina esethandeka kulalowo ololimi olukhohlisayo.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Lowo ontshontshela uyise loba unina athi, “Akusinto embi” ungumngane lomuntu obhidlizayo.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
Umuntu olomhawu ubanga ingxabano, kodwa lowo omethembayo uThixo uzaphumelela.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
Lowo ozithembayo yena uyisiwula, kodwa lowo ohamba ngenhlakanipho uvikelekile.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
Lowo opha abayanga kayikuswela lutho, kodwa ovala amehlo ingathi kababoni uzuza iziqalekiso ezinengi.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Lapho izigangi zisiba yiziphathamandla abantu bayacatsha; kodwa nxa kusifa izixhwali abalungileyo bayaphumelela.

< Karin Magana 28 >