< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Minden istentelen fut, ha senki nem üldözi is; az igazak pedig, mint az ifjú oroszlán, bátrak.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
Az ország bűne miatt sok annak a fejedelme; az eszes és tudós ember által pedig hosszabbodik fennállása.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
A szegény emberből támadott elnyomója a szegényeknek hasonló a pusztító esőhöz, mely nem hágy kenyeret.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
A kik elhagyják a törvényt, dicsérik a latrokat; de a kik megtartják a törvényt, harczolnak azokkal.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
A gonoszságban élő emberek nem értik meg az igazságot; a kik pedig keresik az Urat, mindent megértenek.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Jobb a szegény, a ki jár tökéletesen, mint a kétfelé sántáló istentelen, a ki gazdag.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
A ki megőrzi a törvényt, eszes fiú az; a ki pedig társalkodik a dobzódókkal, gyalázattal illeti atyját.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
A ki öregbíti az ő marháját kamattal és uzsorával, annak gyűjt, a ki könyörül a szegényeken.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
Valaki elfordítja az ő fülét a törvénynek hallásától, annak könyörgése is útálatos.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
A ki elcsábítja az igazakat gonosz útra, vermébe maga esik bele; a tökéletesek pedig örökség szerint bírják a jót.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
Bölcs az ő maga szemei előtt a gazdag ember; de az eszes szegény megvizsgálja őt.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Mikor örvendeznek az igazak, nagy ékesség az; mikor pedig az istentelenek feltámadnak, keresni kell az embert.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
A ki elfedezi az ő vétkeit, nem lesz jó dolga; a ki pedig megvallja és elhagyja, irgalmasságot nyer.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Boldog ember, a ki szüntelen retteg; a ki pedig megkeményíti az ő szívét, bajba esik.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Mint az ordító oroszlán és éhező medve, olyan a szegény népen uralkodó istentelen.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Az értelemben szűkölködő fejedelem nagy elnyomó is; de a ki gyűlöli a hamis nyereséget, meghosszabbítja napjait.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
Az ember, a kit ember-vér terhel, a sírig fut; senki ne támogassa őt.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
A ki jár tökéletesen, megtartatik; a ki pedig álnokul két úton jár, egyszerre elesik.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
A ki munkálja az ő földét, megelégedik étellel; a ki pedig hiábavalóságok után futkos, megelégedik szegénységgel.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
A hivő ember bővelkedik áldásokkal; de a ki hirtelen akar gazdagulni, büntetlen nem marad.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Személyt válogatni nem jó; mert még egy falat kenyérért is vétkezhetik az ember.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
Siet a marhakeresésre a gonosz szemű ember; és nem veszi észre, hogy szükség jő reá.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
A ki megfeddi az embert, végre is inkább kedvességet talál, mint a sima nyelvű.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
A ki megrabolja az atyját, és anyját és azt mondja: nem vétek! társa a romboló embernek.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
A telhetetlen lélek háborúságot szerez; a ki pedig bízik az Úrban, megerősödik.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
A ki bízik magában, bolond az; a ki pedig jár bölcsen, megszabadul.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
A ki ád a szegénynek, nem lesz néki szüksége; a ki pedig elrejti a szemét, megsokasulnak rajta az átkok.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Mikor felemeltetnek az istentelenek, elrejti magát az ember; de mikor azok elvesznek, öregbülnek az igazak.

< Karin Magana 28 >