< Karin Magana 28 >
1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Le méchant fuit sans qu'on le poursuive; mais le juste a de l'assurance comme un jeune lion.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
Quand un pays est en révolte, il a plusieurs chefs; mais le gouvernement est affermi par un homme sage et intelligent.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
Un homme pauvre, qui opprime les petits, est une pluie qui ravage, et fait manquer le pain.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Ceux qui abandonnent la loi, louent les méchants; mais ceux qui gardent la loi, leur font la guerre.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Les gens adonnés au mal n'entendent point ce qui est juste; mais ceux qui cherchent l'Éternel entendent tout.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Le pauvre qui marche dans son intégrité, vaut mieux que celui dont les voies sont détournées et qui est riche.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Celui qui garde la loi est un enfant entendu; mais celui qui se plaît avec les débauchés fait honte à son père.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
Celui qui augmente son bien par intérêt et par usure, l'amasse pour celui qui aura pitié des pauvres.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
Si quelqu'un détourne l'oreille pour ne point écouter la loi, sa prière même est une abomination.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Celui qui fait égarer les hommes droits dans un mauvais chemin, tombera dans la fosse qu'il aura faite; mais les hommes intègres hériteront le bonheur.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
L'homme riche pense être sage; mais le pauvre qui est intelligent le sondera.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Quand les justes se réjouissent, la gloire est grande; mais quand les méchants s'élèvent, chacun se cache.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
Celui qui cache ses transgressions, ne prospérera point; mais celui qui les confesse et qui les abandonne, obtiendra miséricorde.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Heureux est l'homme qui est continuellement dans la crainte; mais celui qui endurcit son cœur tombera dans la calamité.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Un méchant qui domine sur un peuple pauvre est un lion rugissant et un ours affamé.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Le prince qui manque d'intelligence fait beaucoup d'exactions; mais celui qui hait le gain déshonnête, prolongera ses jours.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
L'homme chargé du sang de l'homme fuira jusques à la fosse: que personne ne le retienne!
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Celui qui marche dans l'intégrité trouve le salut; mais celui qui s'en détourne pour suivre deux voies, tombera dans l'une d'elles.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
Celui qui cultive sa terre sera rassasié de pain; mais le compagnon des fainéants sera rassasié de misère.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
L'homme loyal abondera en bénédictions; mais celui qui se hâte de s'enrichir, ne demeurera point impuni.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Il n'est pas bon d'avoir égard à l'apparence des personnes; car pour un morceau de pain un homme fera le mal.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
L'homme envieux se hâte pour s'enrichir, et il ne sait pas que la disette lui arrivera.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
Celui qui reprend quelqu'un, finira par être préféré à celui qui flatte de sa langue.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Celui qui vole son père ou sa mère, et qui dit que ce n'est point un crime, est le compagnon du malfaiteur.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
Celui qui a le cœur enflé excite les querelles; mais celui qui s'assure sur l'Éternel sera rassasié.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
Celui qui se confie en son propre cœur, est un insensé; mais celui qui marche dans la sagesse, sera délivré.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
Celui qui donne au pauvre, n'aura point de disette; mais celui qui en détourne ses yeux, abondera en malédictions.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Quand les méchants s'élèvent, chacun se cache; mais quand ils périssent, les justes se multiplient.